Tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari, ya kasance mutum mai gaskiya da amana da tausayin talakawa.
Mai magana da yawunsa, Garba Shehu, ne ya bayyana hakan a shafinsa na X, a ranar da tsohon shugaban yake murnar cika shekara 82 a rayuwarsa.
Garba Shehu ya ce, “Buhari shugaba ne daban, wanda yake damuwa da damuwar talakawa da masu rauni, sannan yake dagewa wajen inganta rayuwar talakawa da fitar da su daga cikin Ć™unci.”
Garba Shehu ya ce siyasa da cin hanci da rashawa É—anjuma ne da É—anjumai a Ć™asashe da dama, ciki har da Najeriya. “Tunanin mutane shi ne duk É—ansiyasa É—an rashawa ne. Amma shi sunansa “Mai gaskiya” saboda gaskiyarsa da rashin É—aukar duniya da zafi.”
Garba Shehu ya ƙara da cewa Buhari ya yi kamfe ne kan inganta tattalin arziki da samar da tsaro da yaƙi da rashawa.
“A zamanin mulkinsa, Ć™asar ta ga yadda aka É—auki matakai masu yawa domin yaĆ™i da talauci. Buhari ya mayar da hankali kan inganta kiwon lafiya, inda a zamaninsa aka cire Ć™asar daga cikin masu fama da cutar polio,” in ji shi.