fidelitybank

Buhari ne ya hana EFCC ta bincike ni – Osinbajo

Date:

Mataimakin shugaban kasa Farfesa Yemi Osinbajo, ya bayyana cewa shugaban kasa Muhammadu Buhari ya hana shi neman hukumar yaki da yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa EFCC ta binciki zargin zamba da ake yi masa.

Kwamitin wucin gadi na majalisar wakilai kan shirin bada agajin gaggawa da bala’o’i a shekarar 2018 ya tuhumi hukumar gudanarwar hukumar bada agajin gaggawa ta kasa NEMA.

Hukumar wadda Osinbajo ke shugabanta, an zarge ta da amincewa da wani asusun shiga yankin arewa maso gabas na Naira biliyan 5.8 ba bisa ka’ida ba.

Haka kuma a shekarar 2020, an zargi mataimakin shugaban kasar da karbar Naira biliyan 4 daga hannun Ibrahim Magu, tsohon shugaban riko na EFCC.

Osinbajo ya bayyana ikirarin a matsayin “marasa tushe” kuma ya bukaci tsohon sufeto-janar na ‘yan sanda (IGP), Mohammed Adamu, ya binciki zargin.

Da yake magana a ranar Juma’a a wani liyafar cin abinci na sirri don murnar cikar Buhari shekaru 80, Osinbajo ya ce: “Wata rana na je wurinsa saboda akwai wasu zarge-zarge da aka yi mini.

“Na je wurinsa ne domin in nuna masa wasikar da na rubuta wa EFCC domin ta bincika.

“A wannan lokacin ya ce, ‘VP, me yasa kuke damuwa da duk waɗannan mutanen? Wadannan mutane dai suna ta zarge-zarge iri-iri, suna ta yada labarai iri-iri, har ma suna cewa wai zan kara aure. Kuma har wasu wawayen mutane suna jira a Masallacin kasa, suna jira in zo in kara aure,” inji Osinbajo.

daily 
post news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp