Mataimakin shugaban kasa Farfesa Yemi Osinbajo, ya bayyana cewa shugaban kasa Muhammadu Buhari ya hana shi neman hukumar yaki da yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa EFCC ta binciki zargin zamba da ake yi masa.
Kwamitin wucin gadi na majalisar wakilai kan shirin bada agajin gaggawa da bala’o’i a shekarar 2018 ya tuhumi hukumar gudanarwar hukumar bada agajin gaggawa ta kasa NEMA.
Hukumar wadda Osinbajo ke shugabanta, an zarge ta da amincewa da wani asusun shiga yankin arewa maso gabas na Naira biliyan 5.8 ba bisa ka’ida ba.
Haka kuma a shekarar 2020, an zargi mataimakin shugaban kasar da karbar Naira biliyan 4 daga hannun Ibrahim Magu, tsohon shugaban riko na EFCC.
Osinbajo ya bayyana ikirarin a matsayin “marasa tushe” kuma ya bukaci tsohon sufeto-janar na ‘yan sanda (IGP), Mohammed Adamu, ya binciki zargin.
Da yake magana a ranar Juma’a a wani liyafar cin abinci na sirri don murnar cikar Buhari shekaru 80, Osinbajo ya ce: “Wata rana na je wurinsa saboda akwai wasu zarge-zarge da aka yi mini.
“Na je wurinsa ne domin in nuna masa wasikar da na rubuta wa EFCC domin ta bincika.
“A wannan lokacin ya ce, ‘VP, me yasa kuke damuwa da duk waɗannan mutanen? Wadannan mutane dai suna ta zarge-zarge iri-iri, suna ta yada labarai iri-iri, har ma suna cewa wai zan kara aure. Kuma har wasu wawayen mutane suna jira a Masallacin kasa, suna jira in zo in kara aure,” inji Osinbajo.