fidelitybank

Buhari na tattaunawa da masu ruwa da tsaki akan zabe da sauya kudi

Date:

Shugaban kasa Muhammmadu Buhari na jagorantar taron Majalisar Magabata da ke tattauna muhimman batutuwan da kasar ke fama da su a yanzu musamman na sauyin kudi da zabe.

Rahotanni sun nuna cewa daga cikin mahalatta taron a fadarsa da ke Abuja akwai tsofaffin shugabannin kasar da suka hada da Goodluck Jonathan da Yakubu Gowon da Abdulsalami Abubakar da kuma Olusegun Obasanjo da ke halarta ta intanet.

A wurin taron akwai kuma Mataimakin Shugaban Kasa Farfesa Yemi Osinbajo da Shugaban Majalisar Dattawa Ahmad Lawan da Shugaban Majalisar Wakilai Femi Gbajabiamila.

Su kuwa gwamnonin jihohi da ke wurin sun hada da Nasir El-Rufai na Kaduna da Darius Ishaku na Taraba da Babajide Sanwo-Olu na Lagos da kuma Babagana Zulum na Borno.

Wasu gwamnonin da ke halartar taron ta intanet sun hada da Ademola Adeleke na Osun da Abubakar Badaru na Jigawa da Yahaya Bello na Kogi da Atiku Bagudu na Kebbi da Dapo Abiodun na Ogun da Aminu Tambuwal na Sokoto da Simon Lalong na Filato da kuma mataimakan gwamnonin jihar Nasarawa da Bauchi.

Ministan Abuja Mohammed Bello da Sakataren Gwamnatin Tarayya Boss Mustapha da kuma Babban Lauyan gwamnati da Ministan Shari’a Abubakar Malami da kuma Gwamnan Babban Bankin kasar Godwin Emefiele na wurin taron.

Shugaban hukumar zaben Najeriyar, INEC, Mahmood Yakubu wanda shi ma yake zaurn taron ana sa ran zai yi wa majalisar bayani kan shirye-shiryen zabukan da za a fara ranar 25 ga watan nan na Fabarairu.

Dukkanin shugabannin tsaro na Najeriyar kamar yadda tashar talabijin ta Channel ta ruwaito suma suna halartar taron a fadar shugaban kasa.

thisday nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mata da kanan Yara ne Ambaliya ta daidaita a jihohi 19 – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa, NEMA, ta...

Facebook ya ƙi amincewa da tsare-tsaren Turai na amfani da AI

Wasu muhimman tsare-tsare na dokokin Tarayyar Turai kan amfani...

Ranar 18 za a fara rajistar zabe – INEC

Hukumar zaɓe mai zaman kanta, INEC ta sanar da...

Trump ya tura jiragen ruwa na yaki masu dauke da makaman nukiliya kusa da Rasha

Shugaba Trump ya ce, ya umarci a matsar da...

Amnesty na tuhumar gwamnatin Najeriya kan bacewar Dadiyata

Ƙungiyar Amnesty International ta yi Allah-wadai da sakacin da...

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na É—aukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

ÆŠanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa Æ´an Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa Æ´anbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen Æ™auyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faÉ—a ADC

Tsohon É—an jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...
X whatsapp