Shugabanin ƙasashe mambobin ƙungiyar tattalin arzikin ƙasashen Afirka ta yamma na gudanar da taron ƙungiyar karo na 62 a Abuja babban birnin Najeriya.
A wani saƙo da mai taimaka wa shugaban Najeriya kan kafofin sadarwa na zamani Bashir Ahmad ya wallafa a shafinsa Tuwita ta ce, shugabannin za su tattauna batutuwan da suka shafi tsaro da siyasa da tattalin arzikin ƙasashen ƙungiyar.
Tuni dai shugaba Muhammadu Buhari, ya ƙaddamar da aikin ginin sabon sakatariyar ƙungiyar a Abuja.