Tonye Cole, dan takarar gwamna na jamâiyyar All Progressives Congress (APC) a jihar Rivers, ya bukaci shugaban kasa Muhammadu Buhari da ya kafa dokar ta baci a jihar.
Cole ya bayyana cewa, rikicin siyasar da ya dabaibaye jihar ya samo asali ne sakamakon umarnin zartarwa na 21 da 22 da gwamna Nyesom Wike ya sanyawa hannu kwanan nan, jaridar This Day ta ruwaito.
Hakan ya fito ne cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun Sogbeye Eli, kakakin kwamitin yakin neman zaben jamâiyyar APC na 2023 na Ribas, inda Cole ya bukaci shugaban kasar da ya sa baki cikin gaggawa.
âYan adawa a jihar sun ce rikicin da ya addabi jihar ya biyo bayan umarnin Gwamna ne. A cewar Cole, jamâiyyun adawar jihar Ribas a halin yanzu suna cikin kawanya tare da kai hare-hare akai-akai daga âyan daba da âyan daba da ake zargin suna yi wa bangaren gwamna na jamâiyyar PDP aiki.