Kungiyar African Action Congress (AAC), ta yi kira ga shugaban kasa Muhammadu Buhari, da ya kori gwamnan babban bankin Najeriya, Godwin Emefiele daga mukaminsa, saboda tsoma bakinsa a harkokin siyasa.
Hakan na zuwa ne bayan Gwamnan CBN, Emefiele, ya karbi fom din tsayawa takara a jamâiyyar All Progressives Congress.
Rahotanni sun bayyana cewa, Emefiele ya karbi fom ne a ranar Jumaâa daga babban sakataren jamâiyyar a cibiyar taron kasa da kasa (ICC) da ke Abuja.
A cikin wata sanarwa da kakakinta, Femi Adeyeye ya fitar, kungiyar ta AAC ta yi Allah-wadai da siyan âFom na rashin daâaâ inda ya kara da cewa, hakan ya nuna cewa gwamnatin Muhammadu Buhari ta dora cin hanci da rashawa maimakon yakar ta.
AAC ta ci gaba da cewa, dokar ta tabbatar da cewa Emefiele na bayan fastocin, motoci masu dauke da kaya, da kuma jingle da sauran kayan yakin neman zabe da ake yadawa tare da bayyana cewa tabbas ya kasance mamban sirri na jamâiyyar APC.
Jam’iyyar ta kara da cewa “Ta yiwu kawai mu yi cikakken bincike a cikin ayyukanmu na gwamnati don gano adadin ‘ya’yan jam’iyyar APC na sirri da ke kan manyan mukamai da suka haramta bangaranci.”