Abdul Abiola, dan marigayi Kudirat Abiola, ya yi kira ga shugaban kasa Muhammadu Buhari da ya cika alkawarin da ya dauka ta hanyar gurfanar da wadanda suka kashe mahaifiyarsa a gaban kuliya.
Abiola ya bayyana hakan ne a ranar Asabar ta shafin sa na Twitter, @AbdulMKOAbiola.
Ya kuma bukaci shugaban kasar da ya gurfanar da wadanda suka kashe Kudirat, mahaifiyarsa mai shekaru shekaru 44 a duniya, ya kuma kara da cewa, yana da yakinin Buhari ya yi adalci a kan mutuwar mahaifiyarsa.
“A farkon yakin neman zaben ku na shugaban kasa karo na biyu. Na tuna abubuwan da ka faɗa, don haka na sani kai mutum ne mai adalci da gaskiya, saboda haka, na amince da kai.