fidelitybank

Buhari da Tinubu kan su a hade ya ke – Garba Shehu

Date:

Mai magana da yawun tsohon Shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya ce babu wani rashin jituwa tsakanin mai gidansa da Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Mal Garba Shehu, Ya bayyana hakan ne a wata hira da ya yi da BBC game da wani littafi da zai kaddamar a yau Laraba kan irin yadda suka yi aiki da Shugaba Buharin mai taken “According to the President: Lessons from a presidential spokesman’s experience.”

Garba Shehu ya ce akwai jita-jita ce irinta mutane da yaɗ abubuwa da basu da tabbas a kai.

Da aka yi masa tambaya kan me ya sa Buhari baya hallatar taruka ko tsokaci kan wasu abubuwa na gwamnati sai Malam Garba Shehuu ya ce; “Buhari ba mutum ba ne me son shiga abin da bai shafe shi ba, sannan yana da dalilansa na wasu matakan da yake ɗauka idan aka tuntuɓemu za mu ba da amsa”.

Sannan game da littafin da ya rubuta ya ce yana ganin ya kamata mutane su fahimci wane ne Buhari da tsarin ayyukansa, ganin akwai mumunan fahimta da ake yi wa tsohon Shugaban.

Ya ce Allah ya ba shi damar aiki a fadar gwamnati, kuma tsawon shekarun da ya yi na aiki akwai darrusa da dama da suka koya da ya kamata na baya su sa ni.

Sannan matasa da masu karatun jarida akwai abubuwan koyo sosai daga rayuwar Buhari da ayyukansu a fadar gwamati.

Sannan littafi ya bayyana wane ne shugaba Buhari, tsarinsa da yanayin aikinsa, ganin ana yawaita samu masu kushe shi da cewa me ya yi a shekaru takwas da mulkinsa.

Littafi ya yi bayyani kan rayuwarsu ta Villa da fito da bayanai na gaskiya kan wasu zarge-zargen da aka rinka yi wa shugaban, kama daga batun tsaro, diflomasiyya da wasu batutuwa masu muhimmanci.

Ya ce karanta wannan littafi sai sake gamsar da al’umma fahimtar wane ne ainihn tsohon shugaba Buhari.

Sannan ko yanzu da aka ga yana kame jikinsa, kokari ne na ba wa kowa dama da kau da kai, saboda ba ya son shishigi kan wasu lamura da ba su shafe shi fa.

vanguard newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dangote ya rage farashin litar mai zuwa ₦820

Kamfanin matatar man Dangote ya rage farashin litar mai...

Dubai ta sake tsaurara matakan bai wa ‘yan Najeriya biza

Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa, UAE ta sake sanya wasu dokoki...

‘Yan Bindigar Katsina ‘yan asalin jihar mu ne – Gwamna

Gwamnan Katsina Umaru Dikko Radda ya ce galibin 'yan...

Zan yi wa ADC aiki ina cikin jam’iyyar PDP – Sule Lamido

Jigo a babbar jam’iyyar hamayya ta PDP a Najeriya...

Buhari da Tinubu kan su a hade ya ke – Garba Shehu

Mai magana da yawun tsohon Shugaban kasa, Muhammadu Buhari...

Ganduje ya kama aiki a hukumar kula da filayen jirgin sama

Tsohon shugaban jam'iyyar APC mai mulki, Abdullahi Ganduje, ya...

JAMB ta amince da maki 150 mafi ƙanƙanta don samun gurbin karatu a jami’o’i

Hukumar shirya jarrabawar shiga Jami'o'i ta Najeriya (JAMB) ta...

ASUU ta dakatar da yajin aikin da ta fara

Ƙungiyar Malaman Jami'o'i ta Najeriya, ASUU da dakatar yajin...

Masu haɗakar ADC na ɓaɓatu ne saboda rashin gwamnati – Radda

Gwamnan jihar Katsina, Mallam Dikko Umar Radda ya yi...

Ba ruwan Biri da gada a makamin Nukiliya – Shettima

Mataimakin shugaba Najeriya Kashim Shettima ya ce ƙasar za...

An kashe Mutane 70 a jihar Filato

Rahotonni daga jihar Filato na cewa ƴanbindiga sun kai...

Ambaliya ta kashe mutane 100 a Amurka

Hukumomi a jihar Tesxas da ke Amurka sun bayyana...
X whatsapp