fidelitybank

Buhari da Tinubu kan su a hade ya ke – Garba Shehu

Date:

Mai magana da yawun tsohon Shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya ce babu wani rashin jituwa tsakanin mai gidansa da Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Mal Garba Shehu, Ya bayyana hakan ne a wata hira da ya yi da BBC game da wani littafi da zai kaddamar a yau Laraba kan irin yadda suka yi aiki da Shugaba Buharin mai taken “According to the President: Lessons from a presidential spokesman’s experience.”

Garba Shehu ya ce akwai jita-jita ce irinta mutane da yaɗ abubuwa da basu da tabbas a kai.

Da aka yi masa tambaya kan me ya sa Buhari baya hallatar taruka ko tsokaci kan wasu abubuwa na gwamnati sai Malam Garba Shehuu ya ce; “Buhari ba mutum ba ne me son shiga abin da bai shafe shi ba, sannan yana da dalilansa na wasu matakan da yake ɗauka idan aka tuntuɓemu za mu ba da amsa”.

Sannan game da littafin da ya rubuta ya ce yana ganin ya kamata mutane su fahimci wane ne Buhari da tsarin ayyukansa, ganin akwai mumunan fahimta da ake yi wa tsohon Shugaban.

Ya ce Allah ya ba shi damar aiki a fadar gwamnati, kuma tsawon shekarun da ya yi na aiki akwai darrusa da dama da suka koya da ya kamata na baya su sa ni.

Sannan matasa da masu karatun jarida akwai abubuwan koyo sosai daga rayuwar Buhari da ayyukansu a fadar gwamati.

Sannan littafi ya bayyana wane ne shugaba Buhari, tsarinsa da yanayin aikinsa, ganin ana yawaita samu masu kushe shi da cewa me ya yi a shekaru takwas da mulkinsa.

Littafi ya yi bayyani kan rayuwarsu ta Villa da fito da bayanai na gaskiya kan wasu zarge-zargen da aka rinka yi wa shugaban, kama daga batun tsaro, diflomasiyya da wasu batutuwa masu muhimmanci.

Ya ce karanta wannan littafi sai sake gamsar da al’umma fahimtar wane ne ainihn tsohon shugaba Buhari.

Sannan ko yanzu da aka ga yana kame jikinsa, kokari ne na ba wa kowa dama da kau da kai, saboda ba ya son shishigi kan wasu lamura da ba su shafe shi fa.

the sun newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp