Jam’iyar PDP a Najeriya ta ce shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari bai cika alkawari ko daya da ya daukar wa ‘yan Najeriya ba.
Wannan na zuwa ne bayan da shugaban ya yi hira da gidan talabijin na Channels, inda ya bayyana ‘yan jam’iyar adawar a matsayin wadanda su ka gaza.
Hakan ne ya sa PDP ta mayar da martani ta bakin mataimakin jami’in hulda da jama’a na jam’iyar, Ibrahim Abdullahi, wanda ya ce, a jerin alkawuran da Buhari ya dauka daga 2015 zuwa yanzu babu wanda ya cika.
Ya yi ikirarin cewa, daga batun tsaro har zuwa na tattalin arziki ba su ga inda shugaban da jam’iyarsa su ka yi wata nasara da ta wuce abin da gwamnatin PDP da ta shude ta yi ba.