fidelitybank

Bugun Zuciya: Kanin Maradona Hugo ya mutu

Date:

Hugo Maradona wanda kanin fitaccen dan wasan kwallon kafa na Argentina, Diego, ya mutu sakamakon bugun zuciya.

Hugo mai shekaru 52 ya fuskanci bugun zuciyar ne a gidansa da ke Naples. Hugo ya mutu da misalin karfe 11.50 na safiyar Talata.

Hakan na zuwa ne watanni 13 kacal bayan da bugun zuciya ya kashe Diego Maradon, gwarzon gasar cin kofin duniya na Argentina kuma daya daga cikin mafi girma da ya taba buga wasan wanda ya mutu a Argentina a watan Nuwamba 2020 ya na da shekaru 60.

Kafin rasuwar Hugo an hango shi filin wasa na Maradona da ke Naples ta kasar Italiya, domin halartar bikin tunawa da dan uwansa marigayi kuma fitaccen dan wasan kwallon kafa wata daya kacal da ya wuce.

Kafin rasuwar sa ya dai bar mace mai suna Paola Morra, wadda ya aura a shekara ta 2016, tare da ’ya’ya uku.

Ƙananan ‘yan’uwan Maradona da sauran su ne Diego da Raul da Hugo shi ma dan wasan Æ™wallon Æ™afa ne kuma ya sanya hannu tun ya na matsayin matashi ga kungiyar Napoli mai shekaru 18 a 1987.

Amma ba kamar É—an’uwansa ba, wanda ya buga wasa mafi kyawun shekarunsa a Napoli kuma a na girmama shi a birnin Naples ta kasar Italiya a matsayin wani mutum mai daraja.
A ranar 20 ga Satumba, 1987, ‘yan’uwan biyu sun yi wasa da juna tare da Napoli wanda a ka buga 2-1.

Hugo, wanda ya kasance tauraron tawagar Argentina a gasar cin kofin matasa na duniya na FIFA na matasa ‘yan kasa da shekaru 16 a shekarar 1985, wanda ya kasance kan gaba a gasar cin kofin duniya na ‘yan kasa da shekaru 17, ya ci gaba da taka leda a kananun gasa na Spain da Austria da Venezuela kafin ya kawo karshen aikinsa na buga wasa a Japan a karshen shekarun 1990.

Bayan haka ya koma horarwa, kuma ya shiga cikin ajin manyan makarantun matasa a matsayin masu horaswa.

latest news in nigeria 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojojin hadin gwiwa sun hallaka ‘yan Boko Haram a tafkin Chadi

Rundunar hadin gwiwa mai yaƙi da Boko Haram a...

Na yi rashin aboki na gari kuma Najeriya ta rasa mutumin kirki – Tinubu

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, na ci gaba da alhinin...

Shettima ya jagoranci yi wa Buhari addu’o’i na musamman a Daura

An gudanar da addu'o'i na musamman don neman gafara...

Isra’ila ta kashe mana fararen hula – Syria

Shugaban Syria, Ahmed al-Sharaa ya zargi Isra'ila da kai...

Za mu koma fadar gwamnatin Katsina mu karbi gaisuwar Buhari – Radda

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umar Radda ya ce bayan...

Tinubu zai jagoranci yi wa Buhari addu’a

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, zai jagoranci taron addu'o'i na...

MuÆ™arraban Buhari sun ci amanar da ya ba su lokacin mulkinsa – Bagos

Wani tsohon É—an majalisar wakilai, Dachung Bagos ya bayyana...

Guardiola ya bude kofa ga ‘yan wasa shida su bar kungiyar

Kocin Manchester City, Pep Guardiola, a shirye yake ya...

Ba gudu ba ja da baya a zanga-zangar mu – Tsofaffin ‘Yansanda

Kungiyar ‘yan sandan Najeriya masu ritaya ta sanar da...

Malami ya magantu kan sukar rashawa a mulkin marigayi Buhari

Tsohon babban Lauyan Najeriya kuma ministan shari'a, Abubakar Malami,...

Turkiyya ta gargadi Najeriya kan ‘yan ta’addar FETO

Gwamnatin Turkiyya ta fitar da wani gargadin cewa, mambobin...

Kiristoci sun jinjinawa Musulmai yadda aka yi jana’izar Buhari ba kashe kudi

Ana samun karuwar al’ummar Kudancin Najeriya musamman mabiya addinin...
X whatsapp