fidelitybank

Budurwa ta harbe saurayin ta Dan Sanda a jihar Imo

Date:

Rundunar ƴan sanda a jihar Imo ta tabbatar da mutuwar wani jami’inta Cosmos Ugwu sakamakon harbin da budurwarsa ta yi masa.

Budurwar ta harbi Ugwu ranar Talatar da ta gabata. Hukumomi sun bayyana sunanta da Amanda Uchechi Ugo, ƴar asalin ƙaramar hukumar Ahiazu Mbaise wadda shekarunta 23.

Jaridar Punch ta ruwaito daga majiyoyi masu tushe cewa lamarin ya faru a ofishin rundunar da ke Ezinihitte da yammacin ranar rabon kyaututtuka da ake kira Boxing Day a Turancin Ingilishi.

Jami’an da ke aiki a ranar sun ce sun ji harbin bindiga sau uku daga ɗakin marigayin.

“Lokacin da ƴan sanda suka garzaya zuwa ɗakin domin ganin abin da ke faruwa, sai suka ga jami’in mai muƙamin kofur kwance cikin jini.

Wata majiya ta shaida wa jaridar The Punch cewa matashiyar ta harbe shi sau uku a ƙirji da kuma hannunsa na hagu. An garzaya da shi asibitin Evergreen a Ezinihitte, inda likita ya tabbatar ya mutu.”

A yanzu dai matar da ake zargi tana hannun ƴan sanda domin amsa tambayoyi da kuma yiwuwar gurfanarwa a kotu.

Da aka tuntuɓe shi, kakakin rundunar ƴan sanda ta jihar Imo, Henry Okoye ya tabbatar da faruwar al’amarin inda ya ce ƴan sanda suna duk mai yiwuwa domin duba abin da ya faru.

vanguardnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp