Rahotanni sun ce ‘yan ta’addar Boko Haram sun lalata layin Damaturu-Maiduguri mai karfin Kilovolt 330 bayan makonni uku da dawo da shi.
Wani mai sharhi kan harkokin tsaro Zagazola Makama ya bayyana hakan a wani sako da ya wallafa a shafinsa na X ranar Lahadi.
A cewarsa, ‘yan ta’addan sun tarwatsa ma’aikatun TCN da bama-bamai a safiyar ranar Lahadi.
Wannan ci gaban ya jefa Maiduguri da kewaye cikin duhu.
“Maharani sun yi amfani da bama-bamai wajen tarwatsa ginin da misalin karfe biyu na rana, inda suka mayar da Maiduguri da kewaye cikin duhu. Wannan alama ce ta maimaituwa na hare-hare masu mahimmanci daga masu tayar da kayar baya, ”in ji sakon.
Lamarin na zuwa ne makonni bayan da TCN ta maido da layin a ranar 4 ga Satumba, 2024, bayan lalata ta da ‘yan ta’adda suka yi a baya.
A halin da ake ciki, TCN ba ta yi magana a hukumance kan sabon lamarin ba har zuwa lokacin gabatar da wannan rahoto.