fidelitybank

Boko Haram sun kashe mutane uku a Adamawa

Date:

Wasu da ake zargin mayaƙan Boko Haram ne, sun far wa wani ƙauye a jihar Adamawa, inda suka kashe mutum uku tare da lalata kayayyaki da dama.

Mazauna ƙauyen na Dabna da ke karamar hukumar Hong na jihar ne sun ce mayaƙan sun shigo ƙauyen ne kan babura a safiyar ranar Litinin, inda suka yi ta harba bindigogi kan mai uwa da wabi tare da sace kayan abinci da kuma magunguna.

Wani jami’in bijilanti ya ce fararen hula huɗu ne suka mutu a harin, inda ya ƙara da cewa ɗaya daga cikin maharan ya rasa ransa yayin artabu da wasu jami’ansu.

Wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar ƴan sandan jihar Adamawa, Sulaiman Nguroje ya fitar, rundunar sun tabbatar da kai harin, inda suka yi Allah-wadai da shi.

Ya ce ya zuwa yanzu sun tura tawaga zuwa yankin domin kwantar da hankula.

A watan Yulin 2021, wasu da ake zargin ƴan ta-da-ƙayar-baya na Boko Haram suka kaddamar da hari a ƙauyen Dabna tare da kashe mutane da dama.

dailypostnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp