fidelitybank

Boko Haram sun kashe mutane da dama a Yobe

Date:

Wasu da ake tsammanin mayaƙan Boko Haram ne sun kai hari ƙauyen Mafa a ƙaramar Hukumar Tarmuwa da ke jihar Yobe, tare da kashe mutanen da har yanzu ba a san yawansu ba.

Kamfanin dillancin labarai na Najeriya NAN ya rawaito cewa, maharan sun yi sace-sace da yawa tare da banka wa shaguna da gidaje wuta a ƙauyen.

Kakakin ‘yan sanda na jihar Yobe Dungus Abdulkarim ne ya tabbatar da faruwar lamarin a yau Litinin.

“Har yanzu muna aiki ne domin tabbatar da adadin mutanen da suka rasu dalilin wannan hari, wanda aka kai a ranar Lahadi da misalin ƙarfe 4 na yamma.

“Wasu mutane da ake kira Babagana Goni da Bako Ibrahim ne suka shigar da ƙorafi kan harin a ofishin ‘yan sanda da ke Tarmuwa, kuma dukansu mazauna yankin Mafa ne.

“Wasu da ake zargin mayaƙan Boko Haram ne ɗauke da makamai sun kai hari yankin Mafa a kan babura su sama da 50 kuma sun cinna wa shaguna da gidaje da yawa wuta.

Maharan sun kashe mutane da dama, amma har yanzu ba mu ƙididdige adadin waɗanda harin ya shafa ba,” in ji kakakin ‘yan sandan.

Ya ce bayan sun gama kai harin sun bar wasu makamai da rubutun larabci a jikinsu.

A ranar Juma’a NAN ya rawaito cewa, wasu ‘yan bindiga sun kai hari wata makaranta da ke kusa da garin Geidam tare da kashe ɗalibai uku da jikkata ɗaya.

sun newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp