fidelitybank

Boko Haram sun kashe mana dakarun mu 22 a Borno – Sojoji

Date:

Rundunar sojin ƙasar nan ta tabbatar da kisan dakarunta 22 tare da raunata wasu da dama a wani harin ƙunar baƙin wake da mayaƙan Boko Haram suka kai musu a jihar Borno.

Cikin wata sanarwa da daraktan yaɗa labaran shalkwatar tsaron ƙasar, Manyo Janar Edward Buba ya fitar ranar Lahadi ya ce lamarin ya faru ne a lokacin da sojojin suka ƙaddamar da hare-hare kan sansanonin mayaƙan ƙungiyar da ke yankin Timbiktu a jihar.

Ya ƙara da cewa sojojin rundunar Operetion Haɗin Kai’, sun samu nasarar kakkaɓe ‘yantawayen masu yawan gaske a maɓoyarsu a wani hari da suka ƙaddamar musu – tun daga ranar 16 zuwa 25 ga watan Janairu – da nufin murƙushe su.

Manjo Janar Buba ya ce a lokacin harin kakkaɓe sansanonin mayaƙan, sojojin sun samu nasarar kashe mayaƙan ƙungiyar 70, cikin har da wasu manyan fitattun kwamandojin ƙungiyar uku.

”A lokacin kai harin, mayaƙan Boko haram ɗin sun girke abubuwan fashewa da ababen hawa da suka cika da abubuwan fashewa da ‘yan ƙunar baƙin wake domin dakatar da farmakin sojojin.

To sai dai ya ce kasancewar dakarun sojin sun saba da wannan dabara ta mayakan ƙungiyar, sun samu nasarar kauce wa yunƙurin na Boko Haram, ciki har da harbi da jirage marasa matuƙa.

leadership newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp