Wasu da ake zargin mayakan Boko Haram ne sun kai hari ofishin hukumar kwastam da ke garin Geidam a karamar hukumar Geidam a jihar Yobe, inda suka kashe wani jami’in tsaro Usman Gombe.
A cewar wani rahoto, ‘yan ta’addan sun kai farmaki ofishin kwastam da ke kan titin Maine Soroa a cikin motar Golf Volkswagen da kuma wata mota kirar Land Rover da misalin karfe 10:00 na daren ranar Asabar, inda suka fara harbe-harbe.
“Sun kai hari lokacin da suka tabbatar da cewa jami’an Kwastam sun yi ritaya a gida. Cikin firgita da ruwan harsasai, jami’an sun yi ta tururuwa domin tsira da rayukansu; wasu sun tsere ta kofar gidan, yayin da wasu suka sike shingen.
“Abin takaici, an harbe daya daga cikin jami’an, Usman Gombe a lokacin da yake kokarin hawan katanga,” kamar yadda wata majiyar tsaro ta shaida wa Aminiya.
by TaboolaSponsored Links Kuna iya so
Auri ‘yar Kanada kuma Ka Yi Hijira Zuwa Kanada
Kanada IJ
Ya ce maharan sun kuma kona motar sintiri na hukumar Kwastam, da janareta, da wani bangare na ginin ofishin.
“Wannan shi ne karo na biyu da ‘yan Boko Haram ke kashe jami’an Kwastam. A watan da ya gabata mahara sun yi awon gaba da wani jami’i mai suna Babalola da karamin jami’insa, inda daga bisani maharan suka kashe shi,” inji majiyar.
Mazauna garin sun bayyana cewa ayyukan mayakan Boko Haram a wajen Geidam ya karu a ‘yan kwanakin nan.
“Suna karbar haraji daga manoma da makiyaya masu tazarar kilomita kadan daga garin, kuma babu wanda yake yin komai.
“Maimakon haka, jami’an tsaro sun sake tsugunar da shingayen binciken ababen hawa 17 cikin garin inda kuma suka rika biyan ‘yan kasuwar da ke shigo da kayayyaki ta wannan hanya haraji. Muna cikin tsaka mai wuya a wannan garin,” daya daga cikin ‘yan kasuwar ya yi zargin.