fidelitybank

Boko Haram sun kashe jami’in Kwastam a cikin ofishin su na Yobe

Date:

Wasu da ake zargin mayakan Boko Haram ne sun kai hari ofishin hukumar kwastam da ke garin Geidam a karamar hukumar Geidam a jihar Yobe, inda suka kashe wani jami’in tsaro Usman Gombe.

A cewar wani rahoto, ‘yan ta’addan sun kai farmaki ofishin kwastam da ke kan titin Maine Soroa a cikin motar Golf Volkswagen da kuma wata mota kirar Land Rover da misalin karfe 10:00 na daren ranar Asabar, inda suka fara harbe-harbe.

“Sun kai hari lokacin da suka tabbatar da cewa jami’an Kwastam sun yi ritaya a gida. Cikin firgita da ruwan harsasai, jami’an sun yi ta tururuwa domin tsira da rayukansu; wasu sun tsere ta kofar gidan, yayin da wasu suka sike shingen.

“Abin takaici, an harbe daya daga cikin jami’an, Usman Gombe a lokacin da yake kokarin hawan katanga,” kamar yadda wata majiyar tsaro ta shaida wa Aminiya.

by TaboolaSponsored Links Kuna iya so
Auri ‘yar Kanada kuma Ka Yi Hijira Zuwa Kanada
Kanada IJ
Ya ce maharan sun kuma kona motar sintiri na hukumar Kwastam, da janareta, da wani bangare na ginin ofishin.

“Wannan shi ne karo na biyu da ‘yan Boko Haram ke kashe jami’an Kwastam. A watan da ya gabata mahara sun yi awon gaba da wani jami’i mai suna Babalola da karamin jami’insa, inda daga bisani maharan suka kashe shi,” inji majiyar.

Mazauna garin sun bayyana cewa ayyukan mayakan Boko Haram a wajen Geidam ya karu a ‘yan kwanakin nan.

“Suna karbar haraji daga manoma da makiyaya masu tazarar kilomita kadan daga garin, kuma babu wanda yake yin komai.

“Maimakon haka, jami’an tsaro sun sake tsugunar da shingayen binciken ababen hawa 17 cikin garin inda kuma suka rika biyan ‘yan kasuwar da ke shigo da kayayyaki ta wannan hanya haraji. Muna cikin tsaka mai wuya a wannan garin,” daya daga cikin ‘yan kasuwar ya yi zargin.

nasarawa news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...
X whatsapp