fidelitybank

Boko Haram da IS sun kai hari kan jirgin saman sojoji a Borno

Date:

Rahotanni sun bayyana cewa, ‘yan ta’addar Boko Haram da mayakan kungiyar IS a yammacin Afirka sun kai hari a kan wani jirgin sama mai saukar ungulu a rundunar sojoji a jihar Borno a cikin makon da ya gabata.

Naija News ta samu labari cewa, ‘yan ta’addan da ake zargi da alaka da kungiyar Jama’at Ahl as-Sunnah lid-Da’wah Wa’l-Jihād ne suka yi harbin kan wani jirgin sama mai saukar ungulu na rundunar hadin gwiwa ta MNJTF a ranar Alhamis a kokarin da suke yi na kai harin bam da shelikwafta.

Rundunar ta MNJTF wacce ta hada dakaru daga kasashen Benin da Kamaru da Chadi da Nijar da kuma Najeriya na cikin wani shiri lokacin da ‘yan ta’addan suka yi yunkurin tayar da bama-bamai.

Kungiyoyin tsaro dai na da shedikwatarsu a N’Djamena, kuma an dora musu alhakin kawo karshen ta’addancin Boko Haram a cikin wannan kundi.

An tsara rundunar a sassa hudu na kasa: Sector 1 (Cameroon) mai shedikwata a Mora; Sector 2 (Chad) mai shedikwata a Baga-Sola; Sashi na uku (Nigeria) dake garin Baga; da kuma Sector 4 (Niger), dake garin Diffa.

Rahotannin tsaro da aka samu daga Sahara Reporters sun nuna cewa, dan ta’addan ya yi amfani da nagartattun bindigogin kakkabo jiragen sama da kuma GPMG yayin harin da aka kai wa jirgin a ranar Alhamis din da ta gabata.

vanguard newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp