fidelitybank

Boko Haram 263 da iyalansu sun mika wuya ga sojoji

Date:

Rundunar hadin gwiwa ta Multinational Joint Task Force (MNJTF) da ke yaki da ta’addanci a yankin tafkin Chadi ta ce, ‘yan ta’addar Boko Haram 263 da iyalansu sun mika wuya ga sojoji.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Lt.-Col. Abubakar Abdullahi, babban jami’in yada labaran soji na MNJTF a N’djamena, Chadi.

Ya ce maharan sun mika wuya ne tsakanin ranakun 11 ga watan Yuli zuwa 17 ga watan Yulin 2024, yayin da ake ci gaba da gudanar da aikin Operation Lake Sanity II.

“An fara mika wuya ne a ranar 1 ga watan Yuli, lokacin da ‘yan ta’adda biyar suka mika wuya ga dakarun MNJTF a Wulgo, da ke kan iyakar Najeriya da Kamaru.

“Bayanin farko sun nuna wadannan mutane sun fito ne daga Tumbuma da Kutumgulla a karamar hukumar Marte (LGA), Najeriya.

“A wannan rana, Malum Kori Bukar, mai shekaru 50, ya tsere daga maboyar Jibilaram, ya mika kansa ga sojoji.

“Bugu da kari, a ranar 11 ga watan Yuli, ‘yan ta’adda 19 sun mika wuya a kauyen Madaya da ke arewacin kasar Kamaru, sannan wasu 11 sun mika wuya a Wulgo daga maboyar Tumbuma cikin igiyoyi 2.

“A ranar 12 ga Yuli, 2024, mutane 64 sun mika wuya a Bonderi, Kamaru, ciki har da manya maza 6, mata 20, da yara 38. Moreso, a ranar 13 ga Yuli, ‘yan ta’adda 27 sun mika wuya,” in ji shi.

Ya ce binciken farko da aka gudanar ya nuna cewa dukkan mutanen da suka mika wuya na al’ummar Najeriya ne.

“Saboda haka, an mika su ga dakarun Operation HADIN KAI domin ci gaba da daukar mataki,” in ji shi.

mmm.nnn.

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp