fidelitybank

Blinken zai gana da Tinubu a Najeriya

Date:

A yau ne Sakataren harkokin wajen Amurka, Anthony Blinken zai isa Najeriya a wani bangare na rangadin mako daya zuwa kasashen yammacin Afirka hudu.

Amurka na fafutukar ganin dorewar tasirinta yayin da take samun gogayya daga Rasha da China.

Kasashe a yammacin Afirka musamman a yankin Sahel sun fuskanci karuwar matsaloli ciki har da sauye-sauyen gwamnatoci a hudu cikin mambobin kungiyar ECOWA 15.

Ziyarar ta zo ne daidai lokacin da Abuja, babban birnin Najeriya ke fuskantar matsalolin tsaro da sace-sacen jama’a.

Najeriya ta fuskanci karuwar tashin hankali a arewaci da tsakiyar kasar inda yan bindiga ke kai hare-hare tare da satar mutane don kudin fansa.

Kungiyoyi masu ikirarin Jihadi kamar Boko Haram da sauran kungiyoyi masu tafka miyagun laifuka sun kashe daruruwan farar hula tare da daidaita fiye da mutum miliyan biyu a shekarun baya-bayan nan, wani lamari da ke sa shakku game da kokarin da gwamnatin Najeriya take ikirari na kawo sauye-sauye da magance matsalolin tattalin arziki saboda janye tallafin man fetur.

Shugaba Joe Biden na Amurka wanda ke fuskantar kalubale a kudurinsa na sake tsayawa takara, ya yi alkawarin kai ziyara Afirka bara sai dai hakan bai samu ba.

Rangadin da Blinken ke yi na iya zama cikin yunkurin cika alkawarin sai dai yana zuwa ne a lokacin da ake samun sauye-sauyen lamuran siyasa tun ziyararsa ta karshe zuwa yankin a farkon shekarar 2023.

nigerian 
newspapers today the sun

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka Æ´an Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar HaÉ—in kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran Æ™asa za ka mayar da kai ba zaÉ“en 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...
X whatsapp