fidelitybank

Blinken zai gana da Tinubu a Najeriya

Date:

A yau ne Sakataren harkokin wajen Amurka, Anthony Blinken zai isa Najeriya a wani bangare na rangadin mako daya zuwa kasashen yammacin Afirka hudu.

Amurka na fafutukar ganin dorewar tasirinta yayin da take samun gogayya daga Rasha da China.

Kasashe a yammacin Afirka musamman a yankin Sahel sun fuskanci karuwar matsaloli ciki har da sauye-sauyen gwamnatoci a hudu cikin mambobin kungiyar ECOWA 15.

Ziyarar ta zo ne daidai lokacin da Abuja, babban birnin Najeriya ke fuskantar matsalolin tsaro da sace-sacen jama’a.

Najeriya ta fuskanci karuwar tashin hankali a arewaci da tsakiyar kasar inda yan bindiga ke kai hare-hare tare da satar mutane don kudin fansa.

Kungiyoyi masu ikirarin Jihadi kamar Boko Haram da sauran kungiyoyi masu tafka miyagun laifuka sun kashe daruruwan farar hula tare da daidaita fiye da mutum miliyan biyu a shekarun baya-bayan nan, wani lamari da ke sa shakku game da kokarin da gwamnatin Najeriya take ikirari na kawo sauye-sauye da magance matsalolin tattalin arziki saboda janye tallafin man fetur.

Shugaba Joe Biden na Amurka wanda ke fuskantar kalubale a kudurinsa na sake tsayawa takara, ya yi alkawarin kai ziyara Afirka bara sai dai hakan bai samu ba.

Rangadin da Blinken ke yi na iya zama cikin yunkurin cika alkawarin sai dai yana zuwa ne a lokacin da ake samun sauye-sauyen lamuran siyasa tun ziyararsa ta karshe zuwa yankin a farkon shekarar 2023.

taraba state today news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp