fidelitybank

Biyu sun mutu Takwas sun jikkata a wani mumunan hadari a Sokoto – FRSC

Date:

Kwamandan hukumar kiyaye hadurra ta kasa (FRSC) reshen jihar Sokoto, Kaugama Kabo, ya tabbatar da mutuwar mutane biyu a wani hadarin mota da ya rutsa da motoci bakwai.

Kabo ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na kasa NAN, a ranar Asabar cewa, hatsarin ya afku ne da sanyin safiyar Asabar a kauyen Sifawa da ke karamar hukumar Bodinga.

Ya ce, hatsarin ya rutsa da wata motar da ke tafiya inda ta rasa yadda za ta yi, ta kuma taba wasu motoci bakwai ciki har da manyan motoci biyu.

Kabi ya ce, hatsarin ya yi sanadiyar mutuwar mutane biyu yayin da wasu takwas suka samu raunuka daban-daban.

Ya kara da cewa, an kai wadanda suka mutu tare da wadanda suka jikkata zuwa babban asibitin Bodinga.

Kwamandan Sashen ya gargadi direbobin da su guji yin gudu, tuki mai hatsari da sauran munanan halaye da ke jefa rayukan al’umma cikin hadari da lalata dukiyoyi.

tribune

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Isra’ila za ta mayarwa da Iran martani duk da tsagaita wuta

Ministan tsaron Isra'ila, Katz ya bayyana cewa, ya ba...

Ba mu kai wa Isra’ila hari ba – Iran

Kafar watsa labarai ta Iran ta ruwaito gwamnatin ƙasar...

Duk da faduwar farashin mai NNPCL ya kara farashi

Kamfanin man fetur na Najeriya, NNPCL ya ƙara farashin...

Duk wasu Æ™awayen Amurka za su É—anÉ—anar kuÉ—arsu – Iran

Rundunar dakarun juyin juya halin Iran ta fitar da...

Iran ta mayar da martani kan sojojin Amurka dake Qatar

Kafofin yaɗa labaran Iran sun bayyana cewa ƙasar ta...

Faransa ba ta goyon bayan Amurka na kifer da gwamnatin Iran – Barrot

Ministan harkokin wajen Faransa ya ce, ƙasarsu ba ta...

Kotu a Kano ta É—aure masu satar Yara

Babbar kotun jihar Kano da ke zamanta a Miller...

Ba wata hujja da Amurka za ta kai wa Iran hari – Rasha

An gudanar da tattaunawa tsakanin shugaban Rasha Vladimir Putin...

Tinubu ya miÆ™a saÆ™on ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...

Trump ya yaudari Amurkawa da Iran – Aragachi

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya bayyana cewa...

Sai an hukunta Mutanen da suka kashe Æ´an É—aurin aure – Uba Sani

Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya yi Alla-wadai da...
X whatsapp