Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya ce, tsarin biyan kudin makaranta ga daliban sakandiren jihar da ma’aikatar ilimin jihar ta bullo da shi ya ci karo da tsare-tsaren gwamnatin jihar.
A baya dai ma’aikatar ilimin jihar ta fitar da sanarwar da ke cewa daliban sakandire a jihar za su fara biyan kudin makaranta
A wata sanarwa da mataimakin gwamnan na musamman kan harkokin yada labarai Muyiwa Adekeye ya sanya wa hannu gwamnan ya bayyana tsarin ilimi kyauta a matsayin babban burin da gwamnatinsa ta sanya a gaba.
Sanarwar ta ce gwamatin jihar za ta ci gaba da aiwatar da tsarin ilimi kyauta ga daliban sakandire a fadin jihar.