fidelitybank

Birtanya da Amurka ta sake kakabawa Hamas takunkumi

Date:

Birtaniya da Amurka sun sanar da sake kakaba wa Hamas jerin takunkumai zagaye na uku tun bayan harin da ƙungiyar ta kai wa Isra’ila ranar 7 ga watan Oktoba.

Baitulmalin Amurka wanda shi ne ma’aikatar harkokin kuɗin ƙasar na cewa takunkuman za su shafi “manyan kusoshin Hamas da kuma tsare-tsaren da Iran ke samar da tallafi ga Hamas da kuma ƙungiyar Islamic Jihad ta Falasɗinawa” – wadda ita ma wata ƙungiya ce mai gwagwarmaya da makamai a Zirin Gaza.

Kusoshin na fuskantar haramcin tafiye-tafiye da rufe kadarorinsu da kuma hana cinikayyar makamai.

Wasu daga cikin mutanen da takunkuman suka shafa akwai wakilin Islamic Jihad a ƙasar Iran, Naseer Abu Sharif da wani ɗan canji mazaunin Lebanon, wanda ake zargi da gudanar da harkokin tura kuɗi tsakanin Hamas da ƙasar Iran.

nasarawa news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp