fidelitybank

Birtaniya za ta haramta wa ɗalibai kai ƴan uwansu ƙasar

Date:

Birtaniya na shirin haramta wa ɗaliban ƙasar waje masu karatun digiri na biyu zuwa da ‘yan uwansu ƙasar, a yunƙurin gwamnati na rage yawan ‘yan ciranin da ke shiga ƙasar.

An fitar da sanarwar ne kwana biyu kafin alkaluman kididdiga a hukumance da ake sa ran za su nuna cewa waɗanda suka yi hijira zuwa ƙasar sun kai mutum 700,000 a wannan shekara.

A bara, an bai wa mutum 135,788 biza waɗanda ke karkashin kulawar ɗaliban ƙasashen waje, kusan ninki tara a kan adadin da aka bai wa a 2019.

Firaminista Rishi Sunak ya faɗa wa ministoci cewa matakin zai taimaka wajen rage masu ƙaura zuwa ƙasar.

Ya shaida wa majalisar ministocin cewa sauyin da zai fara aiki a watan Janairun 2024, zai taimaka “wajen rage yawan mutane da ke shiga ƙasar,” a cewar fadar gwamnatin Birtaniya.

A makon da ya gabata ya ce ministocin suna “la’akari da zaɓin da suke da shi” na rage yawan ƙaura, amma sun ƙi bayyana matakin da aka amince da shi.

A baya dai jam’iyyar Conservative ta yi alkawarin rage yawan mutanen da ke yin ƙaura zuwa Birtaniya zuwa ƙasa da mutum 100,000 a duk, amma ta yi watsi da manufar gabanin zaɓen 2019 bayan da ta ƙasa cimma burin.

Sanarwar ta ce ba za a sake barin ƴan uwa da kuma abokai na ɗalibai masu karatun digiri na biyu su nemi zama a Birtaniya ba yayin karatunsu, sai dai waɗanda ke karatu a kan kwasa-kwasan da aka keɓe a matsayin na bincike.

A shekarar da ta gabata, an bai wa waɗanda ke karkashin kulawar ɗaliban ƙasashen waje 135,788 biza, wanda ya kai sama da kashi biyar na duk bizar da aka bayar na tallafin karatu, idan aka kwatanta da kashi shida a shekara ta 2019.

Sakatariyar Harkokin Cikin Gida Suella Braverman ta ce ba a taɓa samun ƙaruwar mutanen da ke karkashin ɗaliban da ke karatu da ake bai wa biza ba kamar wannan lokaci,” kuma lokaci ya yi da za a ƙara tsaurara hakan wajen ganin an rage yawan bakin haure. In ji BBC.

A cikin wata sanarwa da ta aike wa majalisar, ta ƙara da cewa matakin zai “kawo daidaito” tsakanin rage ƙaura da “kare fa’idar tattalin arziki da ɗalibai za su iya kawowa Birtaniya”.

legitnewsnigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp