Bayan bin tsare-tsare na sama da shekara 10, a yanzu gwamnatin Birtaniya ta kusan kammala ɗaukar matakan mayar wa Najeriya kuɗin da tsohon gwamnan jihar Delta James Ibori ya sace, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Reuters ta ruwaito.
Reuters ya ambato mai shigar da ƙara na Birtaniya na faɗa wa kotun cewa ƙasar za ta karɓo dala miliyan 129 daga hannun Mista Ibori.
A baya, masu shigar da ƙara sun ce James Ibori ya sace kimamin dala miliyan 165 daga jihar Delta mai arziƙin man fetur ta kudu maso kudancin Najeriya.
Shekara biyu da ta wuce ne, Birtaniya ta mayar wa Najeriya dala miliyan 5.8 da tsohon gwamnan ya sace.
A 2012 ne, aka tusa keyarsa daga Dubai zuwa Birtaniya, inda aka tuhume shi kan laifuka 10 da ke da alaƙa da zambar kuɗi. Bayan ya yi zaman gidan yari na wasu shekaru a Birtaniya, Ibori ya koma Najeriya a 2017.
A cikin wani gajeren saƙo da ya aike wa Reuters, Mista Ibori ya ce zai ɗaukaka ƙara kan umarnin ƙwace kuɗaɗen nasa da kotun ta bayar.
A ranar Juma’a ake sa ran fara mayar da kudin kamar yadda Reuters ya bayyana.
Birtaniya ta samu tsohon gwamnan da laifin satar kuɗaɗen tare da yanke masa hukuncin ɗaurin shekara 13 a gidan yari a shekara ta 2012.
Tsohon gwamnan, ya amsa laifi a gaban kotun London, bisa jerin tuhume-tuhume goma da aka yi masa na haramta kuɗaɗen haram, da kuma haɗa baki domin tafka zamba.
Wannan ne karo na biyu da za a mayar wa Najeriya kuɗaɗen da tsohon gwamnan ya sace, bayan Birtaniya ta mayar wa Najeriya dala miliyan 5.8 a 2021 na almundahanar tsohon gwamnan.
A 2016, gwamnatocin Najeriya da Birtaniya suka sa hannun kan yarjejeniyar mayar da kuɗaden da masu laifi suka sace.