fidelitybank

Birtaniya za ta dawo da kudin da James Ibori ya sace

Date:

Bayan bin tsare-tsare na sama da shekara 10, a yanzu gwamnatin Birtaniya ta kusan kammala ɗaukar matakan mayar wa Najeriya kuɗin da tsohon gwamnan jihar Delta James Ibori ya sace, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Reuters ta ruwaito.

Reuters ya ambato mai shigar da ƙara na Birtaniya na faɗa wa kotun cewa ƙasar za ta karɓo dala miliyan 129 daga hannun Mista Ibori.

A baya, masu shigar da ƙara sun ce James Ibori ya sace kimamin dala miliyan 165 daga jihar Delta mai arziƙin man fetur ta kudu maso kudancin Najeriya.

Shekara biyu da ta wuce ne, Birtaniya ta mayar wa Najeriya dala miliyan 5.8 da tsohon gwamnan ya sace.

A 2012 ne, aka tusa keyarsa daga Dubai zuwa Birtaniya, inda aka tuhume shi kan laifuka 10 da ke da alaƙa da zambar kuɗi. Bayan ya yi zaman gidan yari na wasu shekaru a Birtaniya, Ibori ya koma Najeriya a 2017.

A cikin wani gajeren saƙo da ya aike wa Reuters, Mista Ibori ya ce zai ɗaukaka ƙara kan umarnin ƙwace kuɗaɗen nasa da kotun ta bayar.

A ranar Juma’a ake sa ran fara mayar da kudin kamar yadda Reuters ya bayyana.

Birtaniya ta samu tsohon gwamnan da laifin satar kuɗaɗen tare da yanke masa hukuncin ɗaurin shekara 13 a gidan yari a shekara ta 2012.

Tsohon gwamnan, ya amsa laifi a gaban kotun London, bisa jerin tuhume-tuhume goma da aka yi masa na haramta kuɗaɗen haram, da kuma haɗa baki domin tafka zamba.

Wannan ne karo na biyu da za a mayar wa Najeriya kuɗaɗen da tsohon gwamnan ya sace, bayan Birtaniya ta mayar wa Najeriya dala miliyan 5.8 a 2021 na almundahanar tsohon gwamnan.

A 2016, gwamnatocin Najeriya da Birtaniya suka sa hannun kan yarjejeniyar mayar da kuɗaden da masu laifi suka sace.

punch newspaper headlines today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...
X whatsapp