fidelitybank

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Date:

Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy ta ɗauka na barazanar amincewa da ƙasar Falasɗinu tsantsar goyon baya ne ga ƙungiyar Hamas.

A ranar Talata ne, Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya bayyana cewa ƙasarsa za ta amince da kafa ƙasar Falasɗinu a watan Satumba, matuƙar Isra’ila ba ta dakatar da yaƙi da cika wasu sharuɗɗa ba.

Sai dai Netanyahu ya soki matakin da cewa tamkar nuna goyon baya ne ga abubuwan da Hamas ke yi.

”Starmer ya nuna wa munanan ayyukan Hamas goyin baya ta yadda za ta ci gaba da ayyukanta na ta’addanci da cutar da mutane”, kamar yadda ya wallafa a shafinsa na sada zumunta

Matakin na Birtaniya ya yi kama da na Faransa, wadda ta ce za ta goyi bayan kafa ƙasar Falasɗinu a babban taron Majalisar Ɗinkin Duniya da za a yi a watan Satumba.

Shugaban Falasɗinawa, Mahmoud Abbas, ya yi maraba da wannan ci gaba, amma Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, ya ce hakan zai ƙarfafa Hamas ne kawai.

A halin yanzu dai, har yanzu ana fama da mummunar matsalar jin ƙai a Gaza, inda ake ci gaba da fafatawa.

Masana lafiya da Majalisar Ɗinkin Duniya sun ce yunwa na ƙara tsananta a Gaza.

Yau ne rana ta ƙarshe ta taron kwanaki uku da Majalisar Ɗinkin Duniya ke yi, don neman mafita tsakanin Isra’ila da Falasɗinawa.

national tribune newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...

NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

Babban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya musanta...

Mun samu kuɗin gina titin jirgi daga Maiduguri zuwa Abia – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ce, ta samu duka kuɗin gudanar...

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiɗa wa Isra'ila wasu...
X whatsapp