fidelitybank

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Date:

Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy ta ɗauka na barazanar amincewa da ƙasar Falasɗinu tsantsar goyon baya ne ga ƙungiyar Hamas.

A ranar Talata ne, Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya bayyana cewa ƙasarsa za ta amince da kafa ƙasar Falasɗinu a watan Satumba, matuƙar Isra’ila ba ta dakatar da yaƙi da cika wasu sharuɗɗa ba.

Sai dai Netanyahu ya soki matakin da cewa tamkar nuna goyon baya ne ga abubuwan da Hamas ke yi.

”Starmer ya nuna wa munanan ayyukan Hamas goyin baya ta yadda za ta ci gaba da ayyukanta na ta’addanci da cutar da mutane”, kamar yadda ya wallafa a shafinsa na sada zumunta

Matakin na Birtaniya ya yi kama da na Faransa, wadda ta ce za ta goyi bayan kafa ƙasar Falasɗinu a babban taron Majalisar Ɗinkin Duniya da za a yi a watan Satumba.

Shugaban Falasɗinawa, Mahmoud Abbas, ya yi maraba da wannan ci gaba, amma Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, ya ce hakan zai ƙarfafa Hamas ne kawai.

A halin yanzu dai, har yanzu ana fama da mummunar matsalar jin ƙai a Gaza, inda ake ci gaba da fafatawa.

Masana lafiya da Majalisar Ɗinkin Duniya sun ce yunwa na ƙara tsananta a Gaza.

Yau ne rana ta ƙarshe ta taron kwanaki uku da Majalisar Ɗinkin Duniya ke yi, don neman mafita tsakanin Isra’ila da Falasɗinawa.

nnn-news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp