fidelitybank

Birtaniya ta ci tarar bankin GT dala miliyan 9.3

Date:

Hukumar da ke sa ido kan hada-hadar kuɗi ta Birtaniya ta ci tarar bankin GT dala miliyan 9.3 saboda gazawa a tsare-tsarensa na magance matsalar almundahanar kuɗaɗe.

A wata sanarwa da hukuma ta fitar, ta ce bankin ya gaza a tsarinsa na hana almundahanar kuɗi.

Kamfanin dillacin labari na Reuters ya ruwaito hukumar na cewa bankin ya kasa ɗaukar matakan da suka dace domin magance tsare-tsaren kare almundahanar kuɗaɗe, duk kuwa da irin gargaɗin da aka sha yi masa.

“Bankin da kansa ya gano irin tarin matsalolin da gazawar ke haifarwa, haka mu ma hukumarmu, amma duk da haka bankin bai ɗauki matakan da suka dace ba” kamar yadda sanarwar hukumar hada-hadar kuɗin ƙasar ta bayyana.

Haka kuma hukumar ta ce bankin bai ƙaryata gazawarsa da hukumar ta gano ba, sannan kuma ya amince zai biya tarar.

A wata sanarwa da bankin ya fitar, ya ce ya sasanta da hukumar hada-hadar kuɗin, ya kuma amince da abin da hukumar ta gano na gazawarsa tsakanin watan Oktoban 2014 zuwa Yulin 2019.

Sannan kuma ya amince zai biya tarar kamar yadda hukumar ta buƙata.

daily 
post news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Jihohi 19 da za a yi kwana 9 a na ruwan sama harda Kano – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta yi hasashen za a shafe kwana...

Tinubu ya mika sakon ta’aziyya bisa rasuwar matar MKO Abiola

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya miƙa saƙon ta'aziyyarsa bisa...

Abubuwan da Kwamiti ya gano a wajen Kwamishina mai murabus na Kano

A ranar Litinin ne kwamitin binciken badaƙalar belin Danwawu,...

Bajintar ɗaliban Najeriya a gasar Turanci ta nuna ingancin ilimi a ƙasa – Tinubu

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu, ya taya ƴanmatan nan uku...

Ƙudirin faɗaɗa mamayar Gaza zai ƙara jefa Falasɗinawa cikin hatsari – MDD

Majalisar Ɗinkin Duniya ta bayyana rahotannin da ke kwarmata...

APC a Kano mu na jinjinawa Tinubu – Abdullahi Abbas

Shugabannin jam’iyyar APC a jihar Kano, sun yabawa shugaba...

Kwamishinan da ake tuhuma da belin dilan kwayoyi a Kano ya yi murabus

Kwamishinan Sufuri na Jihar Kano, Ibrahim Ali Namadi ya...

Turji ya saki Mutane 32 bayan zaman sulhu

Shahararren shugaban ‘yan bindiga, Bello Turji, ya saki mutane...

ADC ta gargadi El’Rufa’i kan ruguza jam’iyyar

Shugaban jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) a jihar Kaduna,...

An gindayawa Thomas Partey sharudan beli

An gindaya sharuddan belin tsohon dan wasan tsakiya na...

Fursunoni 37 na jiran zartas musu da hukuncin kisa a Bauchi

Fursunoni 37 da aka yanke wa hukuncin kisa bisa...

Kwamitin sulhu na MDD zai gana kan makomar ƴan Isra’ila da ke hannun Hamas

Kwamitin tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya zai tattauna yau...
X whatsapp