Wani kwamitin majalisar Birtaniya ya nemi gwamnatin Rishi Sunak ta sake duba manufarta ta kasashen waje ta yadda za a iya ayyana China a matsayin bazarana ga Birtaniya.
Kwamitin dake lura da harkokin kasashen waje ya zargi China da satar fasaha, da kuma yi wa ‘yan Birtaniya barazana da kuma daukar tsattsauran mataki kan Taiwan da kuma aiwatar da wasu dokoki masu tsauri wajen habbaka kasar.
A ‘yan kwanakin nan Birtaniya na kallon China a matsayin abokiyar burminta, sai dai mjalisar kasar na son a mayar da zazzafan martani ga Beijing.
Sun nemi Birtaniya ta rage dogaro da China a wasu lamura kamar makamashin tsaro.
Sai dai masana na ganin duk da wadannan korafe-korafe, China wata babbar abokiyar Birtaniya ce ta fuskar kasuwanci da sauyin yanayi.