Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu ya soki shugabannin Faransa da Birtaniya da Canada, bayan sun nemi ya kawo ƙarshen sabbin hare-haren da sojijinsa suka sabunta a Gaza.
Idan kuma ba haka ba, shugabannin uku sun yi barazanar ɗaukan ƙwaƙwaran matakai muddin Isra’ila ta cigaba da nuna kunnen kashi da ƙin ɗage takunkuman hana shigar da kayan agaji Gaza.
Netanyahu ya ce waɗannan kalamai na su tamkar nuna goyon-baya ne ga Hamas.
A jiya Litinnin ne Isra’ila ta sassauta haramcin shigar da kayayyaki a Gaza, sai dai Majalisar Ɗinkin Duniya na cewa hakan da tayi bai wadatar ba.
Ana dai cigaba da luguden bama-bamai babu kakautawa a sassan Gaza.