‘Yan bindiga sun kai hare-hare a karamar hukumar Birnin Gwari da ke jihar Kaduna, sun kashe akalla mutane bakwai, sannan suka yi awon gaba da mutane 57.
Rahotanni sun ce, maharan sun farmaki wata mota a Kuriga, hanyar titin Birnin Gwari zuwa Kaduna a ranar Asabar, 26 ga watan Fabrairu.
Jaridar The Cable ta rawaito cewa, wani dalibin makarantar sakandare ta kimiya da ke Birnin Gwari ya tsere da rauni daga harbin bindiga.
Shugaban kungiyar Birnin Gwari Vanguard for Security and Good Governance, Ibrahim Nagwari, a cikin wani jawabi a ranar Asabar, ya bayyana cewa, maharan sun kuma farmaki mazauna a Unguwar Bula, Unguwar Dafillo da Ijinga a karamar hukumar Randagi.