Binciken ya kuma gano cewa wuraren da aka ajiye rigakafin da kuma karancinsa, da kasancewar an kawo shi Najeriya ya na dab da daina aiki, sun taka muhimmiyar rawa wajen lalacewarsa kafin yin amfanin.
Najeriya dai na da mutane sama da miliyan 200, amma kasa da kaso hudu cikin 100 ne aka yi musu rigakafin cutar, kamar yadda Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta tabbatar.
A cewar binciken, kamfanin AstraZeneca ne ya sarrafa rigakafin, kuma an kawo shi ne daga Turai, ta hanyar tallafin da hadakar kasahe ke ba wa kasashe masu karamin karfi.
Wata majiya ta shaida cewa wasu daga cikin rigakafin an kawo su ne mako hudu zuwa shida kafin lokacin lalacewarsu, kuma ba za a iya amfani da su kafin lokacin ba. A cewar Aminiya.
Majiyar ta kara da cewa har yanzu dai ana ci gaba da kidaya lalatattun rigakafin, kafin a fitar da hakikanin adadinu nan gaba.
Kakakin Hukumar Kula da Lafiya a Matakin Farko ta Kasa, (NPHCDA), ya ce har yanzu hukumar na ci gaba da tattara alkaluman rigakafin da aka shigo da su da wanda aka yi amfani da su kafin ta fitar da alkaluma a nan gaba kadan.
WHO dai ta tabbatar da lalacewar rigakafin, amma ba ta bayar da cikakkun alkaluman hakan ba.