fidelitybank

Binani ta garzaya kotu a ba ta kujerar ta

Date:

Ƴar takarar gwamna a Adamawa ƙarƙashin jam’iyyar APC, Aisha Ɗahiru Binani, ta shigar da ƙara gaban kotu tana neman umarnin wucin gadi game da dambarwa zaɓen jihar.

Tana dai neman Babbar Kotun Tarayya ta Abuja ne ta yi fassarar doka game da matakin da hukumar zaɓe ta ɗauka ranar 16 ga watan Afrilu, bayan an ayyana cewa ita ce ta yi nasarar zama gwamna, a zaɓen 18 ga watan Maris da kuma na cike-giɓi a ranar 15 ga watan Afrilu.

‘Yar takarar tana kuma neman kotu ta ba da umarni sannan ta hana INEC da jami’anta ɗaukar ƙarin wasu matakai na bayyana wanda ya yi nasara a zaɓukan da aka yi, har sai kotun ta yanke hukunci a kan buƙatar yin tsokacin shari’ar.

Mallam Ahmed Sajo, jami’i a kwamitin yaƙin neman zaɓe Sanata Aisha Binani ya shaida wa BBC cewa sun je kotu ne don a yi musu fassarar sashe na 149 na dokar zaɓe ta 2022.

“Sai an mata fassarar ma’anar dokar nan ta zaɓe, sashen da ya ce idan an rigaan ayyana ɗan takara ya ci zaɓe, to sai kotu ce kawai za ta iya warware wannan ayyanawar, ba hukumar zaɓe ko wani mutum ba” in ji Mallam Sajo.

Don haka ƙara na neman kotu ta dakatar da hukumar zaɓe yin duk wani abu har sai ta kammala wannan aiki.

naija hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp