Rundunar ‘yan sandan jihar Borno ta sanya dokar takaita zirga-zirgar ababen hawa na tsawon sa’o’i shida a cikin babban birnin Maiduguri, a wani mataki na tabbatar da tsaro a lokacin bukukuwan Sallah.
Za a kiyaye dokar ne daga karfe 6:00 na safe zuwa 11:00 na safe a ranar Idi a Maiduguri da kewaye.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da kakakin rundunar, ASP Sani Kamilu, ya fitar ranar Asabar a Maiduguri.
Ya ce matakin ba wai don dalilai na tsaro ne kawai ba, a’a don saukaka zirga-zirgar ababen hawa zuwa wuraren sallah.
Sanarwar ta bukaci al’ummar musulmi da su kasance a wuraren da ake gudanar da addu’o’i da wuri-wuri, don gujewa cunkoso, ta kuma shawarci iyaye da su yi taka tsan-tsan wajen kawo matsala a yayin bikin.