fidelitybank

Bikin Sallah: Mun baza jami’ai 862 a Yobe – NSCDC

Date:

Rundunar tsaro ta NSCDC, reshen jihar Yobe, ta tura jami’anta 862 domin tabbatar da gudanar da bukukuwan karamar Sallah babu cikas a jihar.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar, Bala Garba ne ya bayyana hakan ga manema labarai ranar Lahadi a Damaturu.

Garba ya ce kwamandan jihar, Adamu Zakari, ya bayar da umarnin tura jami’an a kananan hukumomi 17 na jihar gabanin bikin Sallah.

“An zabo jami’an ne daga Rundunar Mata, FSF, Counter Terrorist Squad (CTS), Rapid Response Squad (RRS), Anti Vandal Department, Intelligence and Investigations (INTs), Agro Rangers da Operations sashen,” Garba ya bayyana.

Ya kara da cewa an umarce su da su kasance masu himma tare da mutunta mutane yayin gudanar da ayyukansu.

A yayin da ya yaba wa al’ummar jihar kan yadda suka kasance masu bin doka da oda, ya taya daukacin al’ummar musulmi murnar kammala azumin watan Ramadan da kuma bukukuwan Sallah lafiya a gaba.

Ya kuma bukace su da su kai rahoton duk wani motsi na mutane ko wani abu da suka yi kama da su ga hukumar tsaro mafi kusa.

taraba news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp