fidelitybank

Bieber ya sayar da hakkin mallakar wakokinsa dala miliyan 200

Date:

Justin Bieber ya sayar da wani bangare na hakkin mallakar waƙoƙinsa ga kamfanin waƙoƙi na Hipgnosis Songs Capital kan kudin dala miliyan 200.

Yanzu kamfanin ne ke da hakkin mallakar wasu daga cikin waƙoƙin Justin na baya-bayan nan – ciki har da waƙar “Baby” da “Sorry”.

Wannan mataki na nufin kamfanin Hipgnosis zai rika karɓar kudaden sauraren duk wata waƙa da aka saurara a bainar jama’a ta mawakin.

Kamfanin ke da hakkin wallafa wakokin Justin Bieber da suke faifansa mai dauke da waƙoƙi 290.

Wannan ya haɗa da suka waƙoƙinsa da mawallafinsa ya saki gabanin ranar 31 ga watan Disambar 2021.

Babban hakkin mallakar tsarin naɗar waƙoƙin mawaƙin shi ma na cikin wannan tsari.

Kamfanin Hipgnosis bai bayyana sharudan da aka cimma ba a kwantaragin, amma wata majiya ta bayyana wa kamfanin dillancin labarai na AFP cewa darajar kwantaragin ta kai ta dala miliyan 200.

Ana samun ƙaruwar mawakan da ke sayar da haƙƙin mallakarsu ga kamfanonin kiɗe-kiɗe – ciki har da Justin Timberlake da Shakira, waɗanda suma suka cimma yarjejeniyar kwantaragi da kamfanin Hipgnosis.

legit.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...

Mukarraban gwamnati ba zan lamunci dabi’ar zubar da kima ta ba – Abba

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya gargaɗi masu...

WAEC ta sake bude shafinta don duba jarabawar bana

Hukumar shirya jarabawar Afirka ta Yamma (WAEC) ta bayyana...

Indonesia za ta gina asibiti dubu biyu ga Falasɗinawa

Indonesia ta sanar da cewa za ta kafa wata...

Lauyan Sowore ya bukaci a sake shi cikin gaggawa

Lauyoyin ffitaccen ɗan gwagwarmayar nan kuma ɗan jarida, Omoyele...

Najeriya da Indiya za su haɗa kai na yaƙi da fataucin miyagun ƙwayoyi

Hukumar hana sha da fatauncin miyagun ƙwayoyi ta Najeriya,...

Jihohi 19 da za a yi kwana 9 a na ruwan sama harda Kano – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta yi hasashen za a shafe kwana...

Tinubu ya mika sakon ta’aziyya bisa rasuwar matar MKO Abiola

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya miƙa saƙon ta'aziyyarsa bisa...

Abubuwan da Kwamiti ya gano a wajen Kwamishina mai murabus na Kano

A ranar Litinin ne kwamitin binciken badaƙalar belin Danwawu,...
X whatsapp