fidelitybank

Bidiyon kisan Filato da ake yadawa karya ne – Sojoji

Date:

Rundunar Sojin Najeriya ta musanta rahotonnin da ake yaɗawa tare da wani bidiyo a shafukan zumunta cewa dakarunta ne ke wulaƙanta wasu mata a jihar Filtao da ke tsakiyar ƙasar bayan hare-haren ‘yan bindiga.

Rundunar ta ce bidiyon na ɗauke da kanun “Operation Rainbow in Plateau State”, inda a ciki aka ga wasu sojoji na cin zarafin wasu mata.

Wata sanarwa da Birgediya Janar Tukur Gusau ya fitar ta tabbatar da cewa sojojin Najeriya ne a bidiyon amma ba a Filato abin ya faru ba kamar yadda wasu ke yaɗawa.

“Haƙiƙanin gaskiya lamarin ya faru ne a Dajin Sambisa a 2021, kuma matan wasu ne daga cikin abokan zaman mayaƙan Boko Haram a lokacin da aka kama wasu daga cikin garuruwansu,” in ji sanarwar.

Ta ƙara da cewa tuni rundunar ta bincike kuma “ta hukunta waɗanda suka aikata hakan saboda nuna rashin ƙwarewar aiki”.

Wasu daga cikin masu yaɗa bidiyon na nuna cewa lamarin ya faru ne a yankunan Bokkos da Barkin Ladi na jihar Filato bayan ‘yan bindiga sun kai hare-hare tare da kashe mutum kusan 200 lokacin bikin Kirsimeti.

“Muna kira ga masu sake yaɗa wannan bidiyo da su daina yin hakan saboda yana ƙara ta’azzara ƙalubalen tsaron da ake ciki wanda kuma rundunar Operation Safe Heaven ke ƙoƙarin daƙilewa,” a cewar sanarwar.

punch newspaper headlines today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp