Rundunar Sojin Najeriya ta musanta rahotonnin da ake yaɗawa tare da wani bidiyo a shafukan zumunta cewa dakarunta ne ke wulaƙanta wasu mata a jihar Filtao da ke tsakiyar ƙasar bayan hare-haren ‘yan bindiga.
Rundunar ta ce bidiyon na ɗauke da kanun “Operation Rainbow in Plateau State”, inda a ciki aka ga wasu sojoji na cin zarafin wasu mata.
Wata sanarwa da Birgediya Janar Tukur Gusau ya fitar ta tabbatar da cewa sojojin Najeriya ne a bidiyon amma ba a Filato abin ya faru ba kamar yadda wasu ke yaɗawa.
“Haƙiƙanin gaskiya lamarin ya faru ne a Dajin Sambisa a 2021, kuma matan wasu ne daga cikin abokan zaman mayaƙan Boko Haram a lokacin da aka kama wasu daga cikin garuruwansu,” in ji sanarwar.
Ta ƙara da cewa tuni rundunar ta bincike kuma “ta hukunta waɗanda suka aikata hakan saboda nuna rashin ƙwarewar aiki”.
Wasu daga cikin masu yaɗa bidiyon na nuna cewa lamarin ya faru ne a yankunan Bokkos da Barkin Ladi na jihar Filato bayan ‘yan bindiga sun kai hare-hare tare da kashe mutum kusan 200 lokacin bikin Kirsimeti.
“Muna kira ga masu sake yaɗa wannan bidiyo da su daina yin hakan saboda yana ƙara ta’azzara ƙalubalen tsaron da ake ciki wanda kuma rundunar Operation Safe Heaven ke ƙoƙarin daƙilewa,” a cewar sanarwar.