Likitan Fadar White House ya tabbatar da lafiyar Shugaba Joe Biden, inda ya ce yana da kuzarin da zai iya ci gaba da gudanar da ayyukansa a matsayin shugaban ƙasa.
A jiya Alhamis ne likitocin suka shafe sa’a uku suna duba lafiyar shugaban mai shekara tamanin a wani asibiti da ke Washington.
Wannan ne karo na biyu da ake duba lafiyarsa tun bayan da ya hau kan kujerar mulki a 2021.
Ana sa ran nan ba da daɗewa ba Shugaban Amurkar mafi shekaru zai bayyana aniyarsa ta sake neman wa’adi na biyu na shugabancinƙasar.