fidelitybank

Biden ya yi magana da Tinubu a kan sakin jami’in Binance

Date:

Shugaba Bola Tinubu ya tattauna da takwaransa na Amurka Joe Biden ta wayar tarho.

Tattaunawar da aka yi a yau Talata, ta ta’allaka ne kan wani ma’aikacin Binance mai suna Tigran Gambarayan da aka kama da laifin halasta kuɗin haram.

Wata sanarwar da fadar White House ta fitar, ta ce shugabannin ƙasashen biyu sun kuma tattatauna kan karfafa hukumomin tsaro da kuma buƙatar sakin ɗaya daga cikin ma’aikacin kamfanin hada-hadar kuɗin kirifto.

“Shugaba Tinubu ya kuma gode wa Amurka bisa haɗin gwiwa a fannoni daban-daban musamman ma tsaro a Afrika da kuma Afrika ta yamma baki-ɗaya,” in ji sanarwar.

Shugaba Biden ya tabbatar wa Tinubu cewa haɗin gwiwar ƙasashen za ta ci gaba da wanzuwa saboda makomar duniya ta dogara kan Afrika, don haka tana da muhimmanci.

Sun kuma tattauna kan buƙatar bai wa Afrika kujerar dindindin a kwamitin tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya.

Biden ya kuma yi amfani da damar wajen jajantawa Najeriya kan afkuwar iftila’in ambaliya da ya faru a Maiduguri, babban birnin jihar Borno.

today nation

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp