fidelitybank

Biden ya yi magana da Tinubu a kan sakin jami’in Binance

Date:

Shugaba Bola Tinubu ya tattauna da takwaransa na Amurka Joe Biden ta wayar tarho.

Tattaunawar da aka yi a yau Talata, ta ta’allaka ne kan wani ma’aikacin Binance mai suna Tigran Gambarayan da aka kama da laifin halasta kuɗin haram.

Wata sanarwar da fadar White House ta fitar, ta ce shugabannin ƙasashen biyu sun kuma tattatauna kan karfafa hukumomin tsaro da kuma buƙatar sakin ɗaya daga cikin ma’aikacin kamfanin hada-hadar kuɗin kirifto.

“Shugaba Tinubu ya kuma gode wa Amurka bisa haɗin gwiwa a fannoni daban-daban musamman ma tsaro a Afrika da kuma Afrika ta yamma baki-ɗaya,” in ji sanarwar.

Shugaba Biden ya tabbatar wa Tinubu cewa haɗin gwiwar ƙasashen za ta ci gaba da wanzuwa saboda makomar duniya ta dogara kan Afrika, don haka tana da muhimmanci.

Sun kuma tattauna kan buƙatar bai wa Afrika kujerar dindindin a kwamitin tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya.

Biden ya kuma yi amfani da damar wajen jajantawa Najeriya kan afkuwar iftila’in ambaliya da ya faru a Maiduguri, babban birnin jihar Borno.

yola news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...
X whatsapp