fidelitybank

Biden ya gargadi Isra’ila kar su sake su tsokano Iran

Date:

Shugaban Amurka, Joe Biden, ya bukaci Firayim Ministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, da ya yi la’akari da duk wani harin ramuwar gayya da Isra’ila za ta kai kan Iran da sakamakon da hakan zai iya haifar.

A cikin wata tattaunawa ta wayar tarho tsakanin shugabannin biyu, Biden ya bayyana “karara sosai” ga Netanyahu cewa yana bukatar “yin tunani a hankali da dabara game da hadarin da zai iya tasowa”.

Wani babban jami’in gwamnatin Amurka ya bayyana haka a birnin Washington da yammacin Lahadi.

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na NAN cewa, wannan wani abu ne da a kullum ake tattaunawa da bangaren Isra’ila da sauran kawayenta, Biden ya kuma bayyana karara cewa Amurka za ta taimakawa Isra’ila ta kare kanta.

“Isra’ila ta bayyana karara ga gwamnatin Amurka a tattaunawar da ta gabata cewa ba ta neman wani gagarumin ci gaba da Iran.”

Harin kai tsaye da Iran ta kai kan Isra’ila a karshen mako ya kara haifar da fargabar barkewar rikici a Gabas ta Tsakiya.

Tuni dai aka fara yunkurin kasa da kasa a ranar Lahadin da ta gabata don shawo kan lamarin.

Biden da takwarorinsa na kasashe bakwai masu arzikin masana’antu na dimokuradiyya (G7) sun tattauna rikicin tare da yin Allah wadai da wannan babban harin da kakkausar murya.

“Ba ma son ganin wannan ya ta’azzara. Ba mu neman wani babban yaki da Iran, ” John Kirby, daraktan sadarwa na kwamitin tsaron kasa na gwamnatin Amurka, ya ce.

Ya kara da cewa shugaban na Amurka ya fito fili ba ya neman yaki da Iran.

Amurka za ta ci gaba da taimakawa Isra’ila ta kare kanta, in ji Kirby, amma ya ce yadda Isra’ila ta mayar da martani yanzu zai rage nasu.

Amurka dai ta kasance babbar kawa ga Isra’ila kuma babbar mai goyon bayan soji kuma ta sha nanata goyon bayanta yayin da ake takun saka tsakanin Isra’ila da Iran.

Babu tabbas a ranar Lahadi ko Isra’ila za ta mayar da martani ga harin kai tsaye da Iran ta kai a ranar da ta gabata, wanda a cewar majiyoyin Isra’ila, ya hada da makamai masu linzami 300 da jirage marasa matuka.

legit.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu ya gwangwaje tawagar Super Falcons da ruwan daloli da gidaje a Abuja

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bai wa Æ´an wasan...

Super Falcons ta sauka a Abuja tare da yin zagayen nuna kofi

Tawagar Super Falcons ta Najeriya sun isa Abuja bayan...

Za a fuskanci katsewar wutar lantarki a Legas tsawon kwana 25

Masu amfani da wutar lantarki a jihar Legas na...

‘Yan Najeriya ku daina bayar da bayan katin dan kasar ku – NIMC

Hukumar Kula da shaidar ɗan ƙasa (NIMC), ta bayyana...

Likitoci a Legas sun fara yajin aiki saboda rage musu albashi

Ƙungiyar likitoci ta Legas (Medical Guild), wacce ke ƙarƙashin...

Yan Bindiga sun yi wa Mutane 38 yankan Rago a Zamfara

Ƴanbindiga sun kashe wasu mutum 38 ta hanyar yi...

Thailand da Cambodia sun amince da tsagaita wuta

Ƙasashen Thailand da Cambodia sun amince da tsagaita wuta...

Yansanda sun kama Sojoji cikin ‘Æ´an Æ™ungiyar asiri’ a jihar Ogun

Rundunar 'yansanda reshen jihar Ogun, ta tabbatar da kama...

Yadda ambaliya ta shanye Adamawa

Rahotonni daga birnin Yola na jihar Adamawa na cewa,...

Yadda Jodan da Dubai ke jefa wa al’ummar Gaza abinci ta sama

Kafar yaÉ—a labarai ta gwamnatin Jordan ta ce, jiragen...

Tarihi ba zai manta da Najeriya ba a bangaren kwallon kafar Mata

Najeriya ta lashe kofin ƙwallon Afirka na mata karo...

Hogan ya mutu bisa cutar gazawar koda

An bayyana cikakkun bayanai game da mutuwar É—an wasan...
X whatsapp