fidelitybank

Biden ya gargadi Isra’ila kar su sake su tsokano Iran

Date:

Shugaban Amurka, Joe Biden, ya bukaci Firayim Ministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, da ya yi la’akari da duk wani harin ramuwar gayya da Isra’ila za ta kai kan Iran da sakamakon da hakan zai iya haifar.

A cikin wata tattaunawa ta wayar tarho tsakanin shugabannin biyu, Biden ya bayyana “karara sosai” ga Netanyahu cewa yana bukatar “yin tunani a hankali da dabara game da hadarin da zai iya tasowa”.

Wani babban jami’in gwamnatin Amurka ya bayyana haka a birnin Washington da yammacin Lahadi.

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na NAN cewa, wannan wani abu ne da a kullum ake tattaunawa da bangaren Isra’ila da sauran kawayenta, Biden ya kuma bayyana karara cewa Amurka za ta taimakawa Isra’ila ta kare kanta.

“Isra’ila ta bayyana karara ga gwamnatin Amurka a tattaunawar da ta gabata cewa ba ta neman wani gagarumin ci gaba da Iran.”

Harin kai tsaye da Iran ta kai kan Isra’ila a karshen mako ya kara haifar da fargabar barkewar rikici a Gabas ta Tsakiya.

Tuni dai aka fara yunkurin kasa da kasa a ranar Lahadin da ta gabata don shawo kan lamarin.

Biden da takwarorinsa na kasashe bakwai masu arzikin masana’antu na dimokuradiyya (G7) sun tattauna rikicin tare da yin Allah wadai da wannan babban harin da kakkausar murya.

“Ba ma son ganin wannan ya ta’azzara. Ba mu neman wani babban yaki da Iran, ” John Kirby, daraktan sadarwa na kwamitin tsaron kasa na gwamnatin Amurka, ya ce.

Ya kara da cewa shugaban na Amurka ya fito fili ba ya neman yaki da Iran.

Amurka za ta ci gaba da taimakawa Isra’ila ta kare kanta, in ji Kirby, amma ya ce yadda Isra’ila ta mayar da martani yanzu zai rage nasu.

Amurka dai ta kasance babbar kawa ga Isra’ila kuma babbar mai goyon bayan soji kuma ta sha nanata goyon bayanta yayin da ake takun saka tsakanin Isra’ila da Iran.

Babu tabbas a ranar Lahadi ko Isra’ila za ta mayar da martani ga harin kai tsaye da Iran ta kai a ranar da ta gabata, wanda a cewar majiyoyin Isra’ila, ya hada da makamai masu linzami 300 da jirage marasa matuka.

www.leadership ng.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp