fidelitybank

Biden ya ƙaƙaba takunkumai fiye da ɗari biyar a kan Rasha

Date:

Amurka ta sanar da  saboda mamayar da ta yi wa Ukraine da kuma mutuwar madugun adawar ƙasar, Alexei Navalny.

Takunkuman sun shafi mutanen da ke da hannu a tsare Navalny da kuma yaƙin da Rasha take, kamar yadda Shugaba Joe Biden ya sanar.

Za a sa takunkumin hana fitar da kaya kan kusan kamfanoni ko mutane 100.

Tarayyar Turai ta kuma sanar da wasu takunkuman da Rasha ta mayar da martani ta hanyar haramta wa jami’an Tarayyar Turai shiga ƙasarta.

Babu ƙarin bayani kan tasirin da takunkuman za su yi a kan tattalin arzikin Rasha.

Cikin wata sanarwa, Shugaba Biden ya ce takunkuman za su tabbatar shugaban Rasha Vladmir Putin ya ɗanɗana kuɗarsa saboda kama-karyar da yake a cikin gida da kuma fito na fiton dayake da ƙasashe.

Takunkuman na zuwa ne mako ɗaya tun mutuwar fuju’a da Navalny a wani kurkuku da ke yankin Arctic mai tsananin sanyi. Mista Biden ya ce babu tantama kan zargin shugaban na Rasha.

Suna kuma zuwa a jajiberin cika shekara biyu na mamayar da Rasha ta yi wa Ukraine.

“Shekara biyu da ta gabata, ya yi ƙoƙarin ɓatar da Ukraine daga taswira. Idan Putin bai ɗanɗana kuɗarsa ba saboda mutuwarsa da ɓarnar da ya yi, zai ƙara ƙaimi ne,” in ji Mista Biden cikin wata sanarwa.

Tarayyar Turai ta sanar da sa takunkumi kan kusan kamfanoni da mutane ɗari biyu da ake zargin sun taimaka wa Rasha wajen samun makamai da kuma hannu a garkuwa da yaran Ukraine, wani abu da Rasha ta musanta.

A martaninta, ma’aikatar harkokin wajen Rasha ta ce ta faɗaɗa jadawalin sunayen jami’an EU da ƴan siyasar da ta haramta wa shiga ƙasarta.

punch newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp