Tsohuwar kakakin majalisar wakilan Amurka, Nancy Pelosi, ta ɗora alhakin faɗuwar da jam’iyar Democrat ta yi a zaɓen da ya gabata kan shugaba Biden.
Ms Pelosi ta ce inda Biden ya janye daga takara da wuri da Kamala Harris ba ta faɗi zaɓe ba.
Madam Pelosi ta taka muhimmiyar rawa wajen shawo kan Biden na janye takararsa.
Sai dai ta shaida wa jaridar New York Times cewa da ya janye da wuri da jam’iyyar ta samu isasshen lokacin da za ta zaɓo wanda zai maye gurbinsa.
Hakan dai na zuwa ne bayan da Donald Trump ya samu nasara kan ƴar takararsu Kamala Harris a zaɓen.