Wani dan jam’iyyar Democrat a majalisar dokokin Amurka ya ce shugaba Joe Biden ya kasa shaida shi, lokacin da suka hadu a wajen wani taro a watan Yuni, duk da doguwar abotar da ke tsakaninsu.
A wani ra’ayi da ya rubuta a jaridar Boston Globe, Seth Moulton, daga jihar Massachusetts ya jaddada kiran da ya yi wa shugaban a farkon wannan watan cewa ya hakura da sake neman shugabancin kasar saboda yadda shekarunsa suka tura.
Akalla ‘yan jam’iyyar Democrat 30 ne a Majalisa suka bi sahun wannan kira.
Sai dai Mista Biden ya dage cewa shi ne dan takarar da ya fi dacewa ya kayar da Donald Trump.
Ya kuma sanar da aniyarsa ta ci gaba da yaƙin neman zaɓe a mako mai zuwa.
A halin da ake ciki, JD Vance dan takarar mataimakin shugaban kasa na jam’iyyar Republican ya ce idan har shugaban kasar ba shi da koshin lafiyar sake tsayawa takara, to bai kamata ma ya ci gaba da