Nan gaba kaɗan ne shugaban Amirka Joe Biden zai gana da takwaransa na China Xi Jinping a karon farko tun bayan zama shugaban kasa.
Za su tattauna kan batun tsuburin Bali na Indonesia, gabannin taron ƙolin kasashen G20 masu karfin tttalin arziki.
Mai magana da yawun fadar White Hause ya ce abin da shugabannin za su maida hankali a kai shi ne share hanyar alaƙar ƙasashen biyu nan gaba.
Dangantaka tsakanin kasashen na ƙara yin tsami, musamman kan batun mallakar yankin Taiwan ga China.