Kungiyar al’adun gargajiya ta Ohanaeze Ndigbo ta ce, akalla masu fafutukar kafa kasar Biafra 983 ne ke tsare a gidajen gyaran hali daban-daban a kasar nan.
Kungiyar ta bayyana cewa, daga cikin adadin, fursunonin ‘yan kabilar Igbo 182 galibi matasa da mata ne a halin yanzu, suna cikin mawuyacin hali a cibiyar gyaran hali ta Fatakwal kan jiran shari’a kan batun neman kafa kasar Biafra tsakanin shekarar 2016 zuwa 2021.
Mazi Okechukwu Isiguzoro, Sakatare Janar na kungiyar Ohanaeze Ndigbo ta Duniya, a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai jiya, ya bayyana cewa ,“ya zama wajibi mu fadakar da gwamnatin tarayya, domin tabbatar da cewa, duk wani abu da Nnamdi Kanu ya fito na amfani da shi dole ne a mika wa wadannan matasa wadanda laifinsu kawai sanye da kayan Biafra ne. da katin shaida, ko mene ne, wannan shi ne karo na farko da muke magana a madadinsu, kuma sun cancanci a yi musu afuwa kamar Nnamdi Kanu.”