fidelitybank

BEPU ta nesanta kanta a kan kashe mutane biyu a Birnin Gwari

Date:

Ƙungiyar ci gaban al’ummar Birnin Gwari da ke Jihar Kaduna, BEPU ta ce ta damu ƙwarai tare da yin Allah-wadai kan kisan rubdugu da aka yi wa wasu mutum biyu da ake zargin makiyaya ne da ke da alaƙa da ƴan fashin daji.

Ƙungiyar ta BEPU ta nesantar da kanta da yadda aka kashe mutum biyun tare da gargaɗi kan cewa jama’a su daina ɗaukar doka a hannunsu idan ransu ya ɓaci inda ta buƙaci jama’a su rinƙa kai kokensu ga hukumomin da suka dace.

Haka kuma BEPU ta jinjina wa jami’an tsaro da ke ƙoƙarin tabbatar da tsaro a yankin na Birnin Gwari amma duk da haka ta nuna rashin jin daɗinta kan yadda ake bayar da rahotanni marasa daɗi kan Birnin Gwari inda ta ce wasu rahotannin za su iya jefa mazauna ƙaramar hukumar cikin hatsari.

BEPU ta ce gwamnati ta yi gaggawa wurin fitar da sanarwa ba tare da zurfafa bincike ba kan mutanen da aka kashe inda ta ce mutanen da ake zargin makiyaya ne ba makiyaya bane.

Ƙungiyar ta ce bisa bincikenta, waɗanda aka kashen da ake zargin makiyaya ne ba ma ƴan Najeriya bane inda ta ce masu ayyukan ta’addanci ne da suka zo daga Sudan waɗanda kuma suna daga cikin masu kai hare-hare a yankin na Birnin Gwari.

nnn hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

QPC ta nemi INEC ta soke zaɓen Kano

Jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya ta nemi hukumar zaɓe...

Zaɓen Kano: An kama Mutane 288 da tayar da zaune tsaye

Rudunar ƴansandan jihar Kano, ta sanar da kama mutum...

An Kama wakilin jam’iyya da Naira miliyan 25.9 na Siyan Kuri’a

Jami’an tsaro sun kama wani da ake zargin wakilin...

Farashin kayan abinci na rugu-rugu a Najeriya – NBS

Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa (NBS) ta ce hauhawar farashin...

Kotun Kano ta ce a kamo mata Dagacin Tamburawa

Kotun Shari’ar Musulunci da ke shelkwatar Hisbah a Kano,...

Kotu ta ƙwace motocin gwamnatin Zamfara guda 40 daga hannun Matawalle

Kotun Daukaka Kara da ke a Sokoto ta tabbatar...

A na cigaba da gudanar da zaben cike gurbi harda Kano

Kano na ɗaya daga cikin jhihohin da ake kaɗa...

Mutane 12 sun mutu a wani hatsari a Kano – FRSC

Hukumar Kiyaye Haddura ta Ƙasa (FRSC) reshen Kano, ta...

Masarutar Rano ta haramta aurar da Yaran da ba su kammala karatun Firamare ba

Masarautar Rano a Kano ta haramta cire yarinya daga...

Matatar Dangote za ta fara jigilar mai kyauta ga gidajen mai

Matatar man Dangote za ta fara jigilar mai kyauta...

An sassata rikicin da aka shafe shekaru 30 kan Masallacin Sharada da Islamiyya

Tsohon dan takarar gwamnan Kano, Malam Sha’aban Ibrahim Sharada,...

Duk da kalubalen ‘yan siyasa a Kano mun shirya a zaben cike gurbi – INEC

Kwamishinan hukumar zaɓe mai zaman kanta (INEC) reshen jihar...
X whatsapp