fidelitybank

Bazoum ya bayyana a karo na tun bayan hambarar da shi

Date:

Tun bayan juyin mulkin da sojoji suka yi wa Mohamed Bazoum ranar Laraba 26 ga watan Yulin 2023, an ga hamɓararren shugaban tare da Mahamat Idris Deby, shugaban Chadi.

Mahamat Deby ya je Niamey ne a ƙoƙarinsa na shiga tsakanin masu juyin mulkin da kuma ƙungiyar raya tattalin arziƙin Afirka ta Yamma (Ecowas) wadda ta ba wa sojojin Nijar wa’adin kwana bakwai su mayar da Bazoum kan karagar mulki.

Dakarun tsaron fadar shugaban ƙasa ne suka yi wa Bazoum juyin mulki tare da tsare shi a wani sashe na fadar shugaban ƙasar ta Nijar.

Tun daga ranar, ba a ga hamɓararren shugaban a bainar jama’a ba, don haka ba a san taƙamaimai halin da yake ciki ba.

Ƙasashen Yamma da ƙungiyoyin ƙasashe kamar Majalisar Ɗinkin Duniya da Ecowas da Amurka da Faransa har ma da Rasha sun yi ta kira ga sojojin da suka yi juyin mulki a kan su saki Bazoum tare da iyalansa.

daily post nigeria today news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An ceto Mutane 25 da syka kife a kwale-kwalen Sokoto

Hukumomi a jihar Sokoto sun ce, sun samu nasarar...

An fara duba rabon gyaran arzikin Najeriya

Shugaban Hukumar rarraba arziƙin ƙasa RMAFC, Mohammed Shehu, ya...

Kwallaye 6 da aka zurawa Santos a raga ta sanya Neymar ya fashe da kuka

Ɗan wasan tawagar Brazil, Neymar ya fice daga cikin...

Hukumar Shari’a ta magantu kan sadakin dubu 20 da ya yamutsa hazo a Kano

Hukumar shari’a ta jihar Kano, ta ce ba a...

Cutar Mashako ta yi ajalin Yara hudu a Kano

Rahotanni na cewa cutar mashaƙo wadda aka fi sani...

Cin zaben da NNPP ta yi a Kano cuwa-cuwa ne – Ata

Ministan Jiha na Gidaje da Cigaban Birane, Rt Hon...

Mutane kusan 40 sun ɓace sakamakon haɗarin kwale-kwale a Sokoto

Aƙalla mutum 40 ne ake nema bayan haɗarin kwale-kwale...

APC ta yi kwaf daya a zaben cike gurbin Kaduna da Jigawa

Jam'iyyar APC mai mulki a jihar Jigawa ta yi...

Ba mu yarda da zaben Ghari da Tsanyawa ba – NNPP

Jam'iyar NNPP mai mulkin jihar Kano a arewacin Najeriya...

QPC ta nemi INEC ta soke zaɓen Kano

Jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya ta nemi hukumar zaɓe...

Zaɓen Kano: An kama Mutane 288 da tayar da zaune tsaye

Rudunar ƴansandan jihar Kano, ta sanar da kama mutum...

An Kama wakilin jam’iyya da Naira miliyan 25.9 na Siyan Kuri’a

Jami’an tsaro sun kama wani da ake zargin wakilin...
X whatsapp