fidelitybank

Bazoum ne ke da hurumin korar sojojin Faransa – Macron

Date:

Shugaban Faransa, Emmanuel Macron, ya sake tabbatar da cewa gwamnatin mulkin sojan da ta tsige shugaban Nijar Mohamed Bazoum daga kan karagar mulki ba ta da hurumin ba da umurnin janyewar sojojin Faransa daga yankin Sahel na Nijar.

Macron na mayar da martani ne ga sanarwar da gwamnatin mulkin sojan kasar ta yi a ranar 9 ga watan Satumba inda suka zargi Faransa da yin amfani da dabaru na yaudara tare da haddasa tsaiko wajen janye sojojinta 1,500 kamar yadda wani shafin yada labarai mai zaman kansa ActuNiger ya ruwaito.

“Muna cikin Nijar ne domin yakar ta’addanci, bisa bukatar ƙasar da hukumominta da aka zaba, wadanda suka hada da shugaba Bazoum, da gwamnatinsa da majalisar dokokin kasar,” in ji Macron yayin taron G-20 a Indiya.

Ya kuma jaddada cewa, matakin da Faransa ta dauka ya taka muhimmiyar rawa wajen rage hare-haren ta’addanci a Nijar, duk kuwa da hasarar rayukan sojojin Faransa.

Macron ya kuma bayyana cewa, Faransa na haɗa kai da shugabannin kasashen yammacin Afirka domin ganin an sako Bazoum da kuma maido da tsarin mulkin Nijar.

Sabanin haka, shugaban mulkin sojan kasar Birgediya Janar Abdourahmane Tchiane ya zargi Faransa da goyon bayan shirin kungiyar Ecowas na shiga tsakani a Nijar tare da mayar Bazoum kan muƙaminsa.

Ban da haka kuma, wata kungiyar farar hula mai goyon bayan soji mai suna M62 ta shirya wani gagarumin raye-raye a Yamai domin nuna goyon bayansu ga shugabannin sojojin da kuma kiran janyewar sojojin Faransa.

Bikin ya samu halartar jami’an soji da dama wadanda suka godewa magoya bayansu bisa gagarumin taron da suke yi na yakar Faransa

latest news in lokoja, kogi state

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp