fidelitybank

Bayern Munich ta amince ta ɗauki Kane daga Tottenham

Date:

Bayern Munich ta amince za ta sayi dan kwallon Tottenham, Harry Kane kan fam miliyan 86.4.

Kane, mai shekara 30, yana da sauran kunshin kaka daya, wadda za ta kare a karshen wasannin bana, yanzu zabi na wajensa ko zai yadda ya bar Premier League zuwa buga Bundesliga.

Kane shi ne kan gaba a yawan ci wa Tottenham kwallaye a tarihi, mai 280 a raga a wasa 435.

Tun farko an yi ta alakanta Kane da Manchester United a bana, daga baya Bayern Munich ta sanar da cewar tana zawarcin dan kwallon.

Kane ya lashe takalmin zinare karo uku a matakin wanda ci kwallaye da yawa a kakar Premier League, wato, Premier League Golden Boot.

Kane, wanda ya fara buga wa Tottenham tamaula a 2012 ya zama kan gaba a cin kwallaye a Premier League a kakar 2015-16 da 2016-17 da kuma 2020-21.

Kyaftin din tawagar Ingila ya ci kwallo 213 a gasar Premier a wasa 320, saura 48 ya haura Alan Shearer, mai tarihin yawan cin kwallaye a babbar gasar tamaula ta Ingila.

Kane – wanda shi ne kan gaba a yawan ci wa tawagar Ingila kwallaye mai 58 – bai taba daukar wani babban kofi a Tottenham ko a Ingila ba.

Ita kuwa Bayern Munich kan dauki kofuna a kowacce kakar tamaula a Jamus, tana kuma daukar wasu a Turai.

Bayern Munich – wadda a yanzu Thomas Tuchel ke jagoranta – ta dauki Bundesliga na 33 jimilla, kuma a kakar da ta wuce ne ta dauki kofi na 11 a jere.

Zakarun na Jamus na da kofin Zakarun Turai na Champions League shida da kuma German Cup.

besda salary

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp