fidelitybank

Bayern Munich ta amince ta ɗauki Kane daga Tottenham

Date:

Bayern Munich ta amince za ta sayi dan kwallon Tottenham, Harry Kane kan fam miliyan 86.4.

Kane, mai shekara 30, yana da sauran kunshin kaka daya, wadda za ta kare a karshen wasannin bana, yanzu zabi na wajensa ko zai yadda ya bar Premier League zuwa buga Bundesliga.

Kane shi ne kan gaba a yawan ci wa Tottenham kwallaye a tarihi, mai 280 a raga a wasa 435.

Tun farko an yi ta alakanta Kane da Manchester United a bana, daga baya Bayern Munich ta sanar da cewar tana zawarcin dan kwallon.

Kane ya lashe takalmin zinare karo uku a matakin wanda ci kwallaye da yawa a kakar Premier League, wato, Premier League Golden Boot.

Kane, wanda ya fara buga wa Tottenham tamaula a 2012 ya zama kan gaba a cin kwallaye a Premier League a kakar 2015-16 da 2016-17 da kuma 2020-21.

Kyaftin din tawagar Ingila ya ci kwallo 213 a gasar Premier a wasa 320, saura 48 ya haura Alan Shearer, mai tarihin yawan cin kwallaye a babbar gasar tamaula ta Ingila.

Kane – wanda shi ne kan gaba a yawan ci wa tawagar Ingila kwallaye mai 58 – bai taba daukar wani babban kofi a Tottenham ko a Ingila ba.

Ita kuwa Bayern Munich kan dauki kofuna a kowacce kakar tamaula a Jamus, tana kuma daukar wasu a Turai.

Bayern Munich – wadda a yanzu Thomas Tuchel ke jagoranta – ta dauki Bundesliga na 33 jimilla, kuma a kakar da ta wuce ne ta dauki kofi na 11 a jere.

Zakarun na Jamus na da kofin Zakarun Turai na Champions League shida da kuma German Cup.

www.punch news.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ministan harkokin jin ƙai ya zama sabon shugaban jam’iyyar APC na ƙasa

Ministan harkokin jin kai, Farfesa Nentawe Yilwatda, ya zama...

Amurka za ta lalata magungunan takarar haihuwa na dala miliyan 10 da za a kawo Afrika

Gwamnatin Amurka na shirin lalata magungunan tazarar haihuwa da...

Hukumar NAFDAC ta kama abubuwan fashewa a Kano

A cewar hukumar, an gano lita 60,000 na sulphuric...

Sojoji sun fafata da da ‘yan Bindiga a Neja

Rundunar sojiji ta ce, sojoji tare da haɗin gwiwar...

Majalisar Dinkin Duniya za ta dakatar da tallafin abinci a Najeriya

Shirin Abinci na Majalisar Ɗinkin Duniya (WFP) ya bayyana...

Tinubu ya na murkushe ‘Yan adawa – Sule Lamido

Tsohon gwamnan jihar Jigawa, Alhaji Sule Lamido, ya ce...

Gwamnatin Kano ta baiwa yara fifiko – UNICEF

Asusun kula da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya...

Majalisar ta amince da buƙatar Tinubu na ciyo bashin dala biliyan 21

A ranar Talata ne majalisar Dattawa ta amince da...

An sallami Gwamnan Katsina daga asibiti bayan ya samu rauni a hatsarin mota

An sallami gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda,...

Har yanzu Tinubu bai nada Jakadun Najeriya ba – ADC

Jam’iyyar ADC ta soki yadda gwamnatin APC ta shugaba...

Har yanzu ina LP kuma ni ne zan iya saita Najeriya – Datti

Datti Baba-Ahmed, tsohon dan takarar mataimakin shugaban kasa a...

APC ta zama buhun kusa ta gaza a Najeriya – Amaechi

Tsohon gwamnan jihar Ribas, Chibuike Amaechi ya bayyana jam'iyyar...
X whatsapp