fidelitybank

Bayern Munich ta amince ta ɗauki Kane daga Tottenham

Date:

Bayern Munich ta amince za ta sayi dan kwallon Tottenham, Harry Kane kan fam miliyan 86.4.

Kane, mai shekara 30, yana da sauran kunshin kaka daya, wadda za ta kare a karshen wasannin bana, yanzu zabi na wajensa ko zai yadda ya bar Premier League zuwa buga Bundesliga.

Kane shi ne kan gaba a yawan ci wa Tottenham kwallaye a tarihi, mai 280 a raga a wasa 435.

Tun farko an yi ta alakanta Kane da Manchester United a bana, daga baya Bayern Munich ta sanar da cewar tana zawarcin dan kwallon.

Kane ya lashe takalmin zinare karo uku a matakin wanda ci kwallaye da yawa a kakar Premier League, wato, Premier League Golden Boot.

Kane, wanda ya fara buga wa Tottenham tamaula a 2012 ya zama kan gaba a cin kwallaye a Premier League a kakar 2015-16 da 2016-17 da kuma 2020-21.

Kyaftin din tawagar Ingila ya ci kwallo 213 a gasar Premier a wasa 320, saura 48 ya haura Alan Shearer, mai tarihin yawan cin kwallaye a babbar gasar tamaula ta Ingila.

Kane – wanda shi ne kan gaba a yawan ci wa tawagar Ingila kwallaye mai 58 – bai taba daukar wani babban kofi a Tottenham ko a Ingila ba.

Ita kuwa Bayern Munich kan dauki kofuna a kowacce kakar tamaula a Jamus, tana kuma daukar wasu a Turai.

Bayern Munich – wadda a yanzu Thomas Tuchel ke jagoranta – ta dauki Bundesliga na 33 jimilla, kuma a kakar da ta wuce ne ta dauki kofi na 11 a jere.

Zakarun na Jamus na da kofin Zakarun Turai na Champions League shida da kuma German Cup.

vanguard newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojoji sun fafata da da ‘yan Bindiga a Neja

Rundunar sojiji ta ce, sojoji tare da haɗin gwiwar...

Majalisar Dinkin Duniya za ta dakatar da tallafin abinci a Najeriya

Shirin Abinci na Majalisar Ɗinkin Duniya (WFP) ya bayyana...

Tinubu ya na murkushe ‘Yan adawa – Sule Lamido

Tsohon gwamnan jihar Jigawa, Alhaji Sule Lamido, ya ce...

Gwamnatin Kano ta baiwa yara fifiko – UNICEF

Asusun kula da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya...

Majalisar ta amince da buƙatar Tinubu na ciyo bashin dala biliyan 21

A ranar Talata ne majalisar Dattawa ta amince da...

An sallami Gwamnan Katsina daga asibiti bayan ya samu rauni a hatsarin mota

An sallami gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda,...

Har yanzu Tinubu bai nada Jakadun Najeriya ba – ADC

Jam’iyyar ADC ta soki yadda gwamnatin APC ta shugaba...

Har yanzu ina LP kuma ni ne zan iya saita Najeriya – Datti

Datti Baba-Ahmed, tsohon dan takarar mataimakin shugaban kasa a...

APC ta zama buhun kusa ta gaza a Najeriya – Amaechi

Tsohon gwamnan jihar Ribas, Chibuike Amaechi ya bayyana jam'iyyar...

An fara samun takun saka tsakanin Turkiyya da Najeriya a kan kungiyar Gulen

Kungiyar kare hakkin musulmi, MURIC, ta bukaci shugaban kasar...

Arziƙin Najeriya ya ƙaru da kashi 3.13 a farkon 2025 – NBS

Tattalin arzikin Najeriya ya ƙaru da kashi 3.13 cikin...

Kamfanonin lantarki za su katse wutar lantarki saboda bashi

Kamfanonin samar da wutar lantarki, sun ce suna iya...
X whatsapp