Mutane 7 daga Kwanar Dangora da ke karamar hukumar Kiru a jihar Kano, sun mutu a wani hatsarin mota da ya rutsa da su a kan hanyar Kano zuwa Zariya bayan taron gangamin jamâiyyar APC.
Hatsarin kamar yadda wata majiya ta bayyana, ya afku ne da misalin karfe 6 na yamma, lokacin da motar da wadanda abin ya shafa ke ciki ta yi karo da wata tankar mai.
Majiyar ta bayyana cewa mutane biyar ne suka mutu nan take yayin da wasu biyu kuma aka bayyana sun mutu a asibitin Murtala Muhammed.
Ĉan takarar gwamnan ya shiga jimame na mutuwar Kodinetansa a wani hatsari
Ya kara da cewa, “Bayan sun yi karo ne sai motar dakon tankar ta fice daga motar ta murkushe motar Golf a shingen da ke kan hanyar.”
Ya ce wadanda hadarin ya rutsa da su, sun hada da Bala Kariya, Barau Kariya, Hamza Huntu, Danladi Gidan Algaita, Musbahu Gidan Diraman, Yakubu Gidan Diraman da Lawan Gidan Diraman.