Gwamnan jihar Oyo, Seyi Makinde ya ce, za su yi duk mai yiwuwa domin su gyara jam’iyyar PDP, domin ita ce za ta gyara Najeriya.
Makinde ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis a Abuja a lokacin ƙaddamar da kwamitin gwamnoni na jam’iyyar, da kuma fitar da tsare-tsaren cibiyar Peoples Democratic Institute (PDI), wadda cibiya ce ta bincike da aka assasa tun a shekarar 2000 domin bincike da tattara bayanai da horarwa da sauransu, kamar yadda jaridar The Nation ta kalato daga kamfanin dillancin labarai na Najeriya NAN.
Makinde ya ce jam’iyyar ce za ta iya gyara Najeriya, inda ya ƙara da cewa, “za mu gyara PDP, ita kuma sai ta gyara Najeriya.”
Ya ƙara da cewa, “a yanzu da muka fara fuskantar 2027, akwai buƙatar PDP ta samar wa ƴan Najeriya wata damar daban. Ƙasarmu na buƙatar gyara da tsari mai kyau. Ƴan Najeriya na jiran PDP ta kawo musu wani zaɓin,” in ji shi, inda ya ƙara da cewa tun a 1999 yake cin moriyar PDP, sannan ya ce ba zai so ya gurɓata rijiyar da ya sha ruwa a ciki ba.
A nasa jawabin, tsohon shugaban majalisar dattawa, Sanata Bukola Saraki ya nanata buƙatar da ke akwai na haɗin kai a PDP.