fidelitybank

Bayan mun gyara PDP za kuma ta gyara Najeriya – Makinde

Date:

Gwamnan jihar Oyo, Seyi Makinde ya ce, za su yi duk mai yiwuwa domin su gyara jam’iyyar PDP, domin ita ce za ta gyara Najeriya.

Makinde ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis a Abuja a lokacin ƙaddamar da kwamitin gwamnoni na jam’iyyar, da kuma fitar da tsare-tsaren cibiyar Peoples Democratic Institute (PDI), wadda cibiya ce ta bincike da aka assasa tun a shekarar 2000 domin bincike da tattara bayanai da horarwa da sauransu, kamar yadda jaridar The Nation ta kalato daga kamfanin dillancin labarai na Najeriya NAN.

Makinde ya ce jam’iyyar ce za ta iya gyara Najeriya, inda ya ƙara da cewa, “za mu gyara PDP, ita kuma sai ta gyara Najeriya.”

Ya ƙara da cewa, “a yanzu da muka fara fuskantar 2027, akwai buƙatar PDP ta samar wa ƴan Najeriya wata damar daban. Ƙasarmu na buƙatar gyara da tsari mai kyau. Ƴan Najeriya na jiran PDP ta kawo musu wani zaɓin,” in ji shi, inda ya ƙara da cewa tun a 1999 yake cin moriyar PDP, sannan ya ce ba zai so ya gurɓata rijiyar da ya sha ruwa a ciki ba.

A nasa jawabin, tsohon shugaban majalisar dattawa, Sanata Bukola Saraki ya nanata buƙatar da ke akwai na haɗin kai a PDP.

latest news nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp